Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano
Published: April 27, 2026 at 1:42 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tabbatar da nadin Alhaji Murtala Sule Garo a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan jihar, bayan gudanar da tantancewa ta musamman a ranar Litinin.

Wannan mataki ya biyo bayan takardar da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aika wa majalisar, yana neman amincewarsu don cike gurbi na biyu mafi girma a jihar.

A yayin zaman majalisar, mambobin majalisa sun yi wa Hon. Murtala Sule Garo tambayoyi kan gogewarsa da kuma gudunmuwar da yake shirin bayarwa ga gwamnatin jihar. Bayan gamsuwa da bayanansa, majalisar ta amince da shi baki daya.

Gurbin mataimakin gwamnan ya fito ne bayan murabus din tsohon mataimakin gwamna, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo, a ranar 27 ga watan Maris, 2026. Gwarzo ya sauka ne bayan wasu sabani na siyasa da suka shafi canjin shekar gwamnan daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.

Wane Ne Murtala Sule Garo?

Murtala Sule Garo, wanda aka fi sani da “Commander”, ba bako ba ne a siyasar Kano. Ya taba zama Kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautu.

Ya rike mukamin Shugaban Kungiyar Shugabannin Kananan Hukumomi (ALGON) na Kano. Shi ne dan takarar mataimakin gwamna na jam’iyyar APC a zaben 2023.

Wannan nadi ya nuna yadda Gwamna Abba Kabir Yusuf yake kokarin karfafa gwamnatinsa ta hanyar tafiya da jiga-jigan siyasa daga bangarori daban-daban. Masana na ganin cewa gogewar Garo a matakin grassroots zai taimaka wa gwamnatin wajen samun karbuwa a karkara.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci
Next Post: ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
Wasu Yara 50 Sun Kubuta Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai
Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • Shugaba Trump Yace Akwai Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Iran Afrika
  • Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Paparoma Leo: Zai Kai Ziyara Ƙasar Angola Labarai
  • Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027 Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.