Majalisar Dokokin Jihar Kano ta tabbatar da nadin Alhaji Murtala Sule Garo a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan jihar, bayan gudanar da tantancewa ta musamman a ranar Litinin.
Wannan mataki ya biyo bayan takardar da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya aika wa majalisar, yana neman amincewarsu don cike gurbi na biyu mafi girma a jihar.
A yayin zaman majalisar, mambobin majalisa sun yi wa Hon. Murtala Sule Garo tambayoyi kan gogewarsa da kuma gudunmuwar da yake shirin bayarwa ga gwamnatin jihar. Bayan gamsuwa da bayanansa, majalisar ta amince da shi baki daya.
Gurbin mataimakin gwamnan ya fito ne bayan murabus din tsohon mataimakin gwamna, Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo, a ranar 27 ga watan Maris, 2026. Gwarzo ya sauka ne bayan wasu sabani na siyasa da suka shafi canjin shekar gwamnan daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.
Wane Ne Murtala Sule Garo?
Murtala Sule Garo, wanda aka fi sani da “Commander”, ba bako ba ne a siyasar Kano. Ya taba zama Kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautu.
Ya rike mukamin Shugaban Kungiyar Shugabannin Kananan Hukumomi (ALGON) na Kano. Shi ne dan takarar mataimakin gwamna na jam’iyyar APC a zaben 2023.
Wannan nadi ya nuna yadda Gwamna Abba Kabir Yusuf yake kokarin karfafa gwamnatinsa ta hanyar tafiya da jiga-jigan siyasa daga bangarori daban-daban. Masana na ganin cewa gogewar Garo a matakin grassroots zai taimaka wa gwamnatin wajen samun karbuwa a karkara.


