Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna
Published: May 23, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC a jihar Bauchi ta bayyana tsohon gwamnan jihar, Mohammed Abdullahi Abubakar, a matsayin ɗan takararta na gwamna a zaɓen shekarar 2027, bayan nasarar da ya samu a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.

An sanar da sakamakon zaɓen ne da sanyin safiyar Asabar daga bakin shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi, tsohon mataimakin sufeton ‘yan sanda, John Bassey Abang, wanda ya ce an gudanar da zaɓen a ranar Juma’a 22 ga watan Mayun 2026 a faɗin jihar.

A cewarsa, M.A Abubakar SAN ya samu kuri’u dubu 57,517 inda ya doke sauran ‘yan takara shida da suka fafata a zaɓen. Tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya zo na biyu da kuri’u dubu 26,001, yayin da Nura Manu Soro ya samu kuri’u dubu 13,638.

Sauran waɗanda suka shiga takarar sun haɗa da Bala Maijama’a Wunti wanda ya samu kuri’u 13,648, Kabiru Baba Ma’aji mai kuri’u 8,157, Baba Abubakar Suleiman da ya samu kuri’u 7,688, sai Yakubu Yakubu Abdullahi da ya samu kuri’u 7,181.

Da yake bayyana sakamakon, shugaban kwamitin ya ce M.A Abubakar ya cika dukkan sharuɗɗan da ake buƙata, kuma ya samu mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa, saboda haka aka ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi.

Mohammed Abdullahi Abubakar ya taba zama gwamnan Jihar Bauchi tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar APC, kafin ya sha kaye a hannun gwamna mai ci yanzu, Bala Mohammed, na jam’iyyar PDP a zaɓen shekarar 2019.

Nasarar da tsohon gwamnan ya samu na nuni da cewa APC ta fara ɗaukar matakan tunkarar babban zaɓen 2027 a jihar Bauchi, yayin da ake sa ran za a fafata sosai tsakanin manyan jam’iyyun siyasa a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta
Next Post: Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH Afrika
Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawayen Kasar Kwango Ne Suka Kai Hari Filin Jirgin Saman Kisangani Labarai
  • Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
  • Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
  • Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara Afrika
  • Fiorentina Ta Yi Tayin Farko Ga Manchester United Kan Zirkzee Wasanni
  • Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
  • Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri  Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.