Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
Published: May 25, 2026 at 7:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayin da ake shirin gudanar da bikin Eid-el-Kabir na shekarar 2026, wasu shugabannin Kiristoci a Arewacin Najeriya sun fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ga manyan malaman addinin Musulunci da al’ummar Musulmi a sassa daban-daban na duniya domin ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da haƙurin zaman tare tsakanin mabiya addinai.

Babban Faston Cocin Christ Evangelical and Life Intervention Ministry, Fasto Dakta Yohanna Buru, ya taya Musulmi a duniya murnar bikin Eid-el-Kabir.

Ya ce, “Ina taya Musulmi a duk duniya murnar wannan babbar rana. Allah Ya sanya wannan lokaci ya kawo zaman lafiya, farin ciki da arziki ga kowa.”

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, Fasto Buru ya bayyana cewa ya fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ta kafafen sada zumunta zuwa ga abokansa Musulmi, na cikin gida da wajen Najeriya, domin inganta zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

A cewarsa, ya aika da sakonni sama da dubu ɗaya ga abokansa Musulmi a Najeriya da ma ƙasashen waje.

Fasto Buru ya ce bikin Eid-el-Kabir na wannan shekara na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa, matsalolin tsaro da kuma ci gaba da faɗuwar darajar Naira. Ya bayyana cewa raguna ne har yanzu suka fi samun karɓuwa a lokacin bikin, yana mai cewa lokacin Sallah kan samar da ƙarin damar kasuwanci ga masu sayar da dabbobi a gefunan tituna a faɗin Najeriya.

Haka kuma ya miƙa sakon taya murnar Sallah ga Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Sheikh Ibrahim El-Zakzaky; Sheikh Ahmad Gumi; Sheikh Salihu Mai Barota; da Alaramma Ibrahim Musa.

Fasto Buru ya yi addu’ar samun zaman lafiya, ci gaba, tsawon rai da arziki ga Musulmi da iyalansu yayin bikin.

Ya ce, “Barka da Sallah. Allah Ya cika rayuwarku da farin ciki da albarka, kuma Ya sanya alheri da nasara su kasance tare da ku a kullum.”

Ya kuma bayyana cewa wata tawagar haɗin gwiwa ta Musulmi da Kiristoci mai fafutukar zaman lafiya ta kai ziyara wasu kasuwannin dabbobi a Kaduna a karshen mako domin taya ‘yan kasuwa murnar Sallah tare da roƙonsu su rage farashin raguna da sauran dabbobi domin sauƙaƙawa al’umma yayin bikin Sallah.

Hakazalika, Fasto George John ya ce shi ma ya fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ga ‘yan uwansa Musulmi a faɗin Arewacin Najeriya.

Ya ce, “Manufar hakan ita ce ƙarfafa ‘yan uwantaka tare da tunatar da kanmu cewa mu iyali guda ne ƙarƙashin Allah.”

Ya taya Musulmi a duniya murnar Eid-el-Kabir tun kafin ranar bikin, yana addu’ar Allah Ya albarkaci rayuwarsu da ta iyalansu da zaman lafiya, arziki da farin ciki.

“Allah Ya karɓi ibadunku da addu’o’inku. Ina yi muku fatan samun Sallah mai albarka.

Allah Ya cika zukatanku da gidajenku da farin ciki tare da buɗe muku ƙofofin nasara. Eid Mubarak,” in ji Fasto George.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya
Next Post: Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
Kasar Masar Ta Dakatar Da Wasu Ayyukan Da Ake Amfani Da Man Fetur Da Diesel Labarai
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
Kungiyar Tsaro Ta NATO Tana Fuskantar Kalubale Afrika
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira Labarai
  • ‘Yan Jaridar Gidan Gwamnatin Bauchi Sun Kammala Taron Horo Kan Fasahar Sadarwar Zamani Afrika
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
  • Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
  • Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • Kungiyar Kwallon Mata Sun Tsallaka Iyakar Turkiyya Zuwa Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.