Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika

Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
Published: May 25, 2026 at 7:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayin da ake shirin gudanar da bikin Eid-el-Kabir na shekarar 2026, wasu shugabannin Kiristoci a Arewacin Najeriya sun fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ga manyan malaman addinin Musulunci da al’ummar Musulmi a sassa daban-daban na duniya domin ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da haƙurin zaman tare tsakanin mabiya addinai.

Babban Faston Cocin Christ Evangelical and Life Intervention Ministry, Fasto Dakta Yohanna Buru, ya taya Musulmi a duniya murnar bikin Eid-el-Kabir.

Ya ce, “Ina taya Musulmi a duk duniya murnar wannan babbar rana. Allah Ya sanya wannan lokaci ya kawo zaman lafiya, farin ciki da arziki ga kowa.”

Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, Fasto Buru ya bayyana cewa ya fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ta kafafen sada zumunta zuwa ga abokansa Musulmi, na cikin gida da wajen Najeriya, domin inganta zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

A cewarsa, ya aika da sakonni sama da dubu ɗaya ga abokansa Musulmi a Najeriya da ma ƙasashen waje.

Fasto Buru ya ce bikin Eid-el-Kabir na wannan shekara na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa, matsalolin tsaro da kuma ci gaba da faɗuwar darajar Naira. Ya bayyana cewa raguna ne har yanzu suka fi samun karɓuwa a lokacin bikin, yana mai cewa lokacin Sallah kan samar da ƙarin damar kasuwanci ga masu sayar da dabbobi a gefunan tituna a faɗin Najeriya.

Haka kuma ya miƙa sakon taya murnar Sallah ga Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Sheikh Ibrahim El-Zakzaky; Sheikh Ahmad Gumi; Sheikh Salihu Mai Barota; da Alaramma Ibrahim Musa.

Fasto Buru ya yi addu’ar samun zaman lafiya, ci gaba, tsawon rai da arziki ga Musulmi da iyalansu yayin bikin.

Ya ce, “Barka da Sallah. Allah Ya cika rayuwarku da farin ciki da albarka, kuma Ya sanya alheri da nasara su kasance tare da ku a kullum.”

Ya kuma bayyana cewa wata tawagar haɗin gwiwa ta Musulmi da Kiristoci mai fafutukar zaman lafiya ta kai ziyara wasu kasuwannin dabbobi a Kaduna a karshen mako domin taya ‘yan kasuwa murnar Sallah tare da roƙonsu su rage farashin raguna da sauran dabbobi domin sauƙaƙawa al’umma yayin bikin Sallah.

Hakazalika, Fasto George John ya ce shi ma ya fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ga ‘yan uwansa Musulmi a faɗin Arewacin Najeriya.

Ya ce, “Manufar hakan ita ce ƙarfafa ‘yan uwantaka tare da tunatar da kanmu cewa mu iyali guda ne ƙarƙashin Allah.”

Ya taya Musulmi a duniya murnar Eid-el-Kabir tun kafin ranar bikin, yana addu’ar Allah Ya albarkaci rayuwarsu da ta iyalansu da zaman lafiya, arziki da farin ciki.

“Allah Ya karɓi ibadunku da addu’o’inku. Ina yi muku fatan samun Sallah mai albarka.

Allah Ya cika zukatanku da gidajenku da farin ciki tare da buɗe muku ƙofofin nasara. Eid Mubarak,” in ji Fasto George.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya

Karin Labarai Masu Alaka

Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai
Hukumar Kare Hakkin ‘Yan Jarida Tace Isra’ila Ce Ta Kashe ‘Yan Jarida Kashi Biyu Bisa Uku Labarai
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai
Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.