Yayin da ake shirin gudanar da bikin Eid-el-Kabir na shekarar 2026, wasu shugabannin Kiristoci a Arewacin Najeriya sun fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ga manyan malaman addinin Musulunci da al’ummar Musulmi a sassa daban-daban na duniya domin ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da haƙurin zaman tare tsakanin mabiya addinai.
Babban Faston Cocin Christ Evangelical and Life Intervention Ministry, Fasto Dakta Yohanna Buru, ya taya Musulmi a duniya murnar bikin Eid-el-Kabir.
Ya ce, “Ina taya Musulmi a duk duniya murnar wannan babbar rana. Allah Ya sanya wannan lokaci ya kawo zaman lafiya, farin ciki da arziki ga kowa.”
Da yake zantawa da manema labarai a Kaduna, Fasto Buru ya bayyana cewa ya fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ta kafafen sada zumunta zuwa ga abokansa Musulmi, na cikin gida da wajen Najeriya, domin inganta zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.
A cewarsa, ya aika da sakonni sama da dubu ɗaya ga abokansa Musulmi a Najeriya da ma ƙasashen waje.
Fasto Buru ya ce bikin Eid-el-Kabir na wannan shekara na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa, matsalolin tsaro da kuma ci gaba da faɗuwar darajar Naira. Ya bayyana cewa raguna ne har yanzu suka fi samun karɓuwa a lokacin bikin, yana mai cewa lokacin Sallah kan samar da ƙarin damar kasuwanci ga masu sayar da dabbobi a gefunan tituna a faɗin Najeriya.
Haka kuma ya miƙa sakon taya murnar Sallah ga Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar; Sheikh Ibrahim Dahiru Bauchi; Sheikh Ibrahim El-Zakzaky; Sheikh Ahmad Gumi; Sheikh Salihu Mai Barota; da Alaramma Ibrahim Musa.
Fasto Buru ya yi addu’ar samun zaman lafiya, ci gaba, tsawon rai da arziki ga Musulmi da iyalansu yayin bikin.
Ya ce, “Barka da Sallah. Allah Ya cika rayuwarku da farin ciki da albarka, kuma Ya sanya alheri da nasara su kasance tare da ku a kullum.”
Ya kuma bayyana cewa wata tawagar haɗin gwiwa ta Musulmi da Kiristoci mai fafutukar zaman lafiya ta kai ziyara wasu kasuwannin dabbobi a Kaduna a karshen mako domin taya ‘yan kasuwa murnar Sallah tare da roƙonsu su rage farashin raguna da sauran dabbobi domin sauƙaƙawa al’umma yayin bikin Sallah.
Hakazalika, Fasto George John ya ce shi ma ya fara aikewa da sakonnin taya murnar Sallah ga ‘yan uwansa Musulmi a faɗin Arewacin Najeriya.
Ya ce, “Manufar hakan ita ce ƙarfafa ‘yan uwantaka tare da tunatar da kanmu cewa mu iyali guda ne ƙarƙashin Allah.”
Ya taya Musulmi a duniya murnar Eid-el-Kabir tun kafin ranar bikin, yana addu’ar Allah Ya albarkaci rayuwarsu da ta iyalansu da zaman lafiya, arziki da farin ciki.
“Allah Ya karɓi ibadunku da addu’o’inku. Ina yi muku fatan samun Sallah mai albarka.
Allah Ya cika zukatanku da gidajenku da farin ciki tare da buɗe muku ƙofofin nasara. Eid Mubarak,” in ji Fasto George.


