Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC domin tunkarar babban zaben kasa mai zuwa, inda ya bayyana kudirinsa na jagorantar yunkurin farfado da dimokuradiyya, tsaro da tattalin arzikin Najeriya.
Da yake jawabi bayan ayyana shi a matsayin wanda zai wakilci jam’iyyar a zaben shugaban kasa, Atiku ya bayyana godiyarsa ga shugabanni da mambobin ADC bisa amincewar da suka nuna masa.
Ya ce jam’iyyar ADC ta nuna cewa dimokuradiyya na nan daram a Najeriya, duk da abin da ya kira matsin lamba da takurawa jam’iyyun adawa daga gwamnatin APC mai mulki.
Atiku ya ce a cikin ADC ana bai wa mambobi damar bayyana ra’ayoyinsu da fafatawa cikin gaskiya da adalci, yana mai cewa hakan ya bambanta da yadda ake gudanar da siyasa a yanzu.
Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya zargi gwamnatin tarayya da haddasa rikice-rikice a jam’iyyun adawa ta hanyar amfani da hukumomin gwamnati da wasu bangarori na shari’a.
Ya kuma yi Allah wadai da ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, , yana mai cewa ana amfani da tsare-tsare irin haka wajen tsoratar da ‘yan adawa.
Atiku ya ce gwamnatin ADC idan ta hau mulki za ta dauki matakai masu tsauri wajen magance matsalar rashin tsaro ta hanyar karfafa rundunonin tsaro, samar da kayan aiki na zamani, horas da jami’ai da kuma inganta walwalarsu.
A bangaren ilimi kuwa, ya yi alkawarin samar da ilimin firamare da sakandare kyauta tare da bai wa matasa horo kan fasahar zamani, kirkire-kirkire da sana’o’i domin rage zaman banza da rashin aikin yi.
Dangane da tattalin arziki, Atiku ya soki gwamnatin APC kan yadda talauci da wahalar rayuwa suka karu a kasar, yana mai cewa gwamnatin sa za ta mayar da hankali wajen samar da ci gaban tattalin arziki mai anfani ga daukacin ‘yan Najeriya.
Ya kuma yi alkawarin ba bangaren lafiya muhimmanci ta hanyar kara zuba jari a cibiyoyin kiwon lafiya da samar da asibitoci na zamani domin rage tafiye-tafiyen neman magani zuwa kasashen waje.
Atiku ya yi kira ga dukkan mambobin jam’iyyar da sauran ‘yan siyasa masu kishin kasa da su hada kai domin tabbatar da nasarar jam’iyyar a babban zaben kasa mai zuwa.


