An shiga jimami a jihar Gombe bayan rasuwar dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gombe, Kwami da Funakaye a Majalisar Wakilan Tarayya, Yaya Bauchi Tongo, wanda ya rasu a birnin Abuja bayan fama da rashin lafiya na wani lokaci.
Rasuwar tasa ta haifar da alhini a tsakanin iyalansa, abokan siyasa, magoya baya da daukacin al’ummar jihar Gombe, musamman ma al’ummar mazabar da yake wakilta.
Marigayin ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan siyasa a jihar Gombe, inda ya yi fice wajen wakiltar al’ummarsa da kuma kokarin kawo ayyukan ci gaba da tallafa wa mabukata a mazabarsa.
A cikin sakon ta’aziyya da ya fitar, gwamnan ya bayyana marigayin a matsayin gogaggen dan siyasa mai tushe a tsakanin al’umma, kuma jajirtaccen mai hidimar jama’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummarsa da jiharsa hidima.
Gwamna Inuwa Yahaya ya ce rasuwar Tongo babban rashi ne ba ga iyalansa da al’ummar mazabarsa kadai ba, har ma ga daukacin Jihar Gombe da Najeriya baki daya.
Ya ce marigayin ya yi fice wajen aiwatar da ayyukan raya mazaba, tallafa wa mabukata da kuma kokarin inganta rayuwar al’ummar da yake wakilta a majalisar dokokin tarayya.
A cewar gwamnan, Yaya Bauchi Tongo ya kasance shugaba mai kusanci da jama’a, wanda gudummawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma da hidimar kasa ta sa ya samu karbuwa da girmamawa daga mutane da dama.
Gwamnan ya kuma tuna da irin gudummawar da marigayin ya bayar a mukamai daban-daban da ya rike, yana mai cewa za a ci gaba da tunawa da shi saboda tawali’unsa, saukin kai da kuma jajircewarsa wajen bunkasa rayuwar al’ummar mazabarsa.
Ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, al’ummar mazabar Gombe/Kwami/Funakaye, Shugaban Majalisar Wakilai ta Najeriya, , ‘yan majalisar dokoki ta kasa, abokan siyasa da kuma daukacin al’ummar Jihar Gombe.
Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin, Ya sanya shi a Aljannatul Firdausi tare da bai wa iyalansa da masoyansa hakurin jure wannan babban rashi.


