Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika

Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya
Published: June 13, 2026 at 6:04 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An shiga jimami a jihar Gombe bayan rasuwar dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gombe, Kwami da Funakaye a Majalisar Wakilan Tarayya, Yaya Bauchi Tongo, wanda ya rasu a birnin Abuja bayan fama da rashin lafiya na wani lokaci.

Rasuwar tasa ta haifar da alhini a tsakanin iyalansa, abokan siyasa, magoya baya da daukacin al’ummar jihar Gombe, musamman ma al’ummar mazabar da yake wakilta.

Marigayin ya kasance daya daga cikin fitattun ‘yan siyasa a jihar Gombe, inda ya yi fice wajen wakiltar al’ummarsa da kuma kokarin kawo ayyukan ci gaba da tallafa wa mabukata a mazabarsa.

A cikin sakon ta’aziyya da ya fitar, gwamnan ya bayyana marigayin a matsayin gogaggen dan siyasa mai tushe a tsakanin al’umma, kuma jajirtaccen mai hidimar jama’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummarsa da jiharsa hidima.

Gwamna Inuwa Yahaya ya ce rasuwar Tongo babban rashi ne ba ga iyalansa da al’ummar mazabarsa kadai ba, har ma ga daukacin Jihar Gombe da Najeriya baki daya.

Ya ce marigayin ya yi fice wajen aiwatar da ayyukan raya mazaba, tallafa wa mabukata da kuma kokarin inganta rayuwar al’ummar da yake wakilta a majalisar dokokin tarayya.

A cewar gwamnan, Yaya Bauchi Tongo ya kasance shugaba mai kusanci da jama’a, wanda gudummawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma da hidimar kasa ta sa ya samu karbuwa da girmamawa daga mutane da dama.

Gwamnan ya kuma tuna da irin gudummawar da marigayin ya bayar a mukamai daban-daban da ya rike, yana mai cewa za a ci gaba da tunawa da shi saboda tawali’unsa, saukin kai da kuma jajircewarsa wajen bunkasa rayuwar al’ummar mazabarsa.

Ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan marigayin, al’ummar mazabar Gombe/Kwami/Funakaye, Shugaban Majalisar Wakilai ta Najeriya, , ‘yan majalisar dokoki ta kasa, abokan siyasa da kuma daukacin al’ummar Jihar Gombe.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin, Ya sanya shi a Aljannatul Firdausi tare da bai wa iyalansa da masoyansa hakurin jure wannan babban rashi.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
Next Post: Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
Gwamnatin Tarayya: Bikin Al’adun Argungu Ya Karbu A Idon Duniya Labarai
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
  • Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
  • Shugaba Tinubu Ya Yabawa Dakarun Tsaro Bisa Ceto Matar Marigayi Janar Rabe
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci
  • Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Ansamu Maganin Da Yake Rage Kitsen Jijiyoyi A Amurka Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Ayyana Dokar-Ta-Baci A Fannin Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.