Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye Afrika
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika

Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC
Published: June 27, 2026 at 7:10 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi da na kansiloli a zaben kananan hukumomin Jihar Gombe da aka gudanar a ranar Asabar a kananan hukumomi 11 da kuma Sabbin Gundumomin Ci Gaba na Kananan Hukumomi (LCDAs) guda 13 na jihar.

Da yake bayyana sakamakon zaben a Gombe, Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Jihar Gombe (GOSIEC), Alhaji Garba Abdu Talasse, ya ce jam’iyyu shida ne suka shiga zaben.

Jam’iyyun sun hada da African Action Congress (AAC), All Progressives Congress (APC), Democratic Leadership Alliance (DLA), National Rescue Movement (NRM), Youth Party (YP), da Zenith Labour Party (ZLP).

Alhaji Talasse ya bayyana cewa duk da cewa jam’iyyun shida sun shiga zaben, ba dukkansu ne suka tsayar da ‘yan takara a kowace kujerar da aka fafata ba.

Ya bayyana yadda aka gudanar da zaben a matsayin mai cike da zaman lafiya, tsari da nasara.

A cewarsa, jam’iyyar APC ta lashe dukkan kujerun shugabannin kananan hukumomi 24 da aka fafata a kananan hukumomi 11 da kuma LCDAs 13 na jihar.

Hakazalika, jam’iyyar ta samu nasarar lashe dukkan kujerun kansiloli 240 da aka fafata a fadin jihar.

Shugaban GOSIEC, Alhaji Garba Abdu Talasse, ya yaba wa al’ummar Jihar Gombe saboda yadda suka gudanar da kansu cikin lumana yayin zaben.

Ya kuma gode wa Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, bisa samar da yanayi mai kyau da kuma goyon bayan da ya bayar wanda ya taimaka wajen gudanar da zaben cikin nasara.

Haka nan ya yaba wa dukkan jam’iyyun siyasa da masu sa ido kan zabe saboda gudummawar da suka bayar wajen tabbatar da cewa an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da nasara.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika
Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jam’iyyu Shida Sun Shiga Zaben Kananan Hukumomin Gombe – GOSIEC
  • Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye
  • Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano! Najeriya
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.