Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya buɗe taron Jigawa State Investment Summit 2026 da aka gudanar a Dutse, inda ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki matakai masu wahala amma masu muhimmanci domin dawo da tattalin arzikin ƙasa kan turbar bunƙasa mai ɗorewa.
A jawabin da ya gabatar, Shettima ya bayyana wasu daga cikin dabarun da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa domin sauƙaƙa harkokin kasuwanci da zuba jari a Najeriya.

Ya ce ta hanyar Presidential Enabling Business Environment Council (PEBEC) da kuma sauye-sauyen tsarin tattalin arziki da kuɗi, gwamnatin tarayya ta maye gurbin shingayen gudanarwa da haɗin gwiwa, lamarin da ya bai wa jihohi damar bunƙasa tattalin arzikinsu da jawo masu zuba jari.


