Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe da ke arewa maso gabashin Najeriya ta sanar da ceto wani yaro mai shekara takwas da aka sace, tare da kama mutum huɗu da ake zargi da hannu wajen aikata laifin.
A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, an fara bincike ne bayan iyalan yaron sun kai rahoton ɓacewarsa ga ‘yan sanda a Ƙaramar Hukumar Akko.
Binciken da jami’an tsaro suka gudanar ya kai ga cafke wani da ake zargi a Kumo, wanda daga bisani ya taimaka wajen kamo wasu mutum uku da ake zargi da haɗa baki wajen sace yaron.
Rundunar ta ce an gano yaron a hannun waɗanda ake zargin, inda aka ceto shi cikin ƙoshin lafiya ba tare da ya samu wani rauni ba, sannan aka miƙa shi ga iyalansa.
‘Yan sandan sun bayyana cewa bincike kan lamarin na ci gaba, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.
Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya yaba da ƙwarewar jami’an da suka gudanar da aikin, tare da yin kira ga jama’a su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin taimakawa wajen yaƙi da aikata laifuka.


