Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass
Published: July 5, 2026 at 4:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tawagar masu yaɗa labarai da ke halartar shirin Arewa Media Summit ta kai ziyara zuwa aikin gina Kano Northern Bypass, a ci gaba da rangadin manyan ayyukan gwamnatin tarayya da ake aiwatarwa a Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Rangadin ya gudana ne bisa jagorancin Ofishin Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Malam Abdulaziz Abdulaziz, domin bai wa mahalarta taron damar ganin ci gaban ayyukan raya ƙasa da gwamnatin tarayya ke gudanarwa a Arewacin Najeriya.

Aikin Kano Northern Bypass, mai tsawon kusan kilomita 38, ya taso daga hanyar Kano–Hadejia zuwa hanyar Kano–Katsina. Ana sa ran kammala aikin zai rage cunkoson manyan motoci da ke bi ta cikin birnin Kano tare da sauƙaƙa zirga-zirgar kayayyaki da fasinjoji.

Masana sun bayyana cewa aikin zai rage asarar lokaci da kuɗaɗen sufuri, ya bunƙasa harkokin kasuwanci da masana’antu, tare da ƙara jawo masu zuba jari zuwa yankunan Zaura, Dawanau, Tarda da sauran al’ummomin da ke kewaye da hanyar.

Haka kuma, ana hasashen aikin zai samar da sabbin guraben ayyukan yi ga matasa da kuma ƙarfafa tattalin arzikin jihar da ma yankin Arewa baki ɗaya.

Masu shirya Arewa Media Summit sun ce rangadin na ba ‘yan jarida da masu tasiri a kafafen sada zumunta damar ganin ayyukan da ido, domin su samar wa al’umma sahihan rahotanni masu dogaro da hujjoji kan ci gaban da ake samu a ƙarƙashin Ajandar Renewed Hope ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ana sa ran taron Arewa Media Summit zai gudana ranar 6 ga Yulin 2026 a Coronation Hall da ke Gidan Gwamnatin jihar Kano, inda zai haɗa manyan ‘yan jarida, masana, masu tasiri da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna rawar kafafen yaɗa labarai wajen bunƙasa ci gaban Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: An Binne Gawar Tsohon Shugaban Sashen Hausa Na VOA, Leo Keyen
Next Post: Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
  • ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau Afrika
  • Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84 Afrika
  • Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
  • Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
  • Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.