Gwamnatin Tarayya ta buƙaci masu tasiri a kafafen sada zumunta da sauran masu yaɗa bayanai su riƙa tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa, tana mai jaddada cewa yaɗa labaran ƙarya na iya haifar da rikice-rikice tare da barazana ga zaman lafiya da ci gaban ƙasa.
Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Abdulaziz Abdulaziz, ne ya bayyana hakan a jawabin maraba da ya gabatar yayin buɗe taron farko na Arewa Media Summit, wanda aka gudanar a ranar Litinin a Kano.

Ya ce bunƙasar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa na buƙatar amincewa da haɗin kai tsakanin gwamnati, kafafen yaɗa labarai da kuma al’umma, yana mai cewa taron ya tattaro shugabanni, ‘yan jarida, masu ƙirƙirar abubuwan da ake wallafawa a shafukan sada zumunta, masu tasiri da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna hanyoyin ƙarfafa alaƙar gwamnati da jama’a ta hanyar gaskiya, riƙon amana da ɗabi’ar aikin jarida.
Abdulaziz ya bayyana cewa taken taron, “Government-Citizen Accord: Accountability, Responsibility and Ethical Media Practice,” ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar sake gina amincewa tsakanin gwamnati da al’umma.
A cewarsa, gwamnati na da alhakin samar da sahihan bayanai cikin buɗaɗɗen tsari, yayin da al’umma ke da nauyin tabbatar da gaskiyar bayanai kafin yaɗa su, tare da riƙe gwamnati da alhakin ayyukanta ta hanyar lumana da bin doka.
Ya ƙara da cewa kafafen yaɗa labarai su ne gada tsakanin gwamnati da jama’a, yana mai cewa ingantaccen aikin jarida da tabbatar da sahihancin labarai na taka muhimmiyar rawa wajen gina zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa.
Ya jaddada cewa masu tasiri a shafukan sada zumunta sun zama manyan masu yaɗa bayanai a wannan zamani, don haka wajibi ne su riƙa tantance gaskiyar bayanai kafin wallafawa.

«”A yau, saƙon da aka wallafa na iya haifar da fata ko kuma tayar da husuma cikin ɗan lokaci. Don haka bai kamata neman farin jini ko yawan masu kallo ya zama sanadin jefa ƙasa cikin rikici ba,” in ji shi.»
Abdulaziz ya kuma yi kira ga masu amfani da kafafen sada zumunta su taka rawar gani wajen kare zaman lafiyar ƙasa yayin da zaɓen shekarar 2027 ke ƙaratowa, tare da gyara duk wani kuskure idan ya faru.
Ya bayyana cewa a wani ɓangare na shirye-shiryen taron, an horas da sama da mutum 100 daga cikin masu goyon bayan jam’iyyar APC da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan dabarun yaɗa bayanai da kuma bayyana manufofi da nasarorin gwamnati yadda ya kamata.
Haka kuma, ya sanar da ƙaddamar da shirin Gani-Ya-Kori-Ji, wanda zai zagaya jihohin Arewacin Najeriya domin haska ayyukan ci gaba da Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi suka aiwatar, musamman waɗanda ba su samu isasshen haske daga kafafen yaɗa labarai ba.
A cewarsa, taron ya nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kare ‘yancin faɗin albarkacin baki, ƙarfafa tattaunawa da bunƙasa dimokuraɗiyya.
Ya ce an tsara taron ne domin bai wa masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na Arewacin Najeriya damar tattaunawa kan yadda za a inganta alaƙar gwamnati da jama’a.
A ƙarshe, Abdulaziz ya yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa karɓar baƙuncin taron, yana mai bayyana Kano a matsayin cibiyar siyasa, kasuwanci da tattaunawa a Najeriya.
Ya kuma buƙaci mahalarta taron su fito da shawarwari da sabbin alƙawurra da za su inganta buɗaɗɗen tsarin mulki, ƙarfafa ɗabi’ar aikin jarida da kuma bunƙasa kyakkyawar alaƙa tsakanin gwamnati da al’umma.


