Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Tantance Gaskiyar Bayanai Shi Ne Ginshiƙin Aikin Jarida Mai Nagarta – Abdulaziz
Published: July 6, 2026 at 5:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci masu tasiri a kafafen sada zumunta da sauran masu yaɗa bayanai su riƙa tantance sahihancin bayanai kafin wallafawa, tana mai jaddada cewa yaɗa labaran ƙarya na iya haifar da rikice-rikice tare da barazana ga zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa na Musamman kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Abdulaziz Abdulaziz, ne ya bayyana hakan a jawabin maraba da ya gabatar yayin buɗe taron farko na Arewa Media Summit, wanda aka gudanar a ranar Litinin a Kano.

Ya ce bunƙasar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa na buƙatar amincewa da haɗin kai tsakanin gwamnati, kafafen yaɗa labarai da kuma al’umma, yana mai cewa taron ya tattaro shugabanni, ‘yan jarida, masu ƙirƙirar abubuwan da ake wallafawa a shafukan sada zumunta, masu tasiri da sauran masu ruwa da tsaki domin tattauna hanyoyin ƙarfafa alaƙar gwamnati da jama’a ta hanyar gaskiya, riƙon amana da ɗabi’ar aikin jarida.

Abdulaziz ya bayyana cewa taken taron, “Government-Citizen Accord: Accountability, Responsibility and Ethical Media Practice,” ya zo a daidai lokacin da ake buƙatar sake gina amincewa tsakanin gwamnati da al’umma.

A cewarsa, gwamnati na da alhakin samar da sahihan bayanai cikin buɗaɗɗen tsari, yayin da al’umma ke da nauyin tabbatar da gaskiyar bayanai kafin yaɗa su, tare da riƙe gwamnati da alhakin ayyukanta ta hanyar lumana da bin doka.

Ya ƙara da cewa kafafen yaɗa labarai su ne gada tsakanin gwamnati da jama’a, yana mai cewa ingantaccen aikin jarida da tabbatar da sahihancin labarai na taka muhimmiyar rawa wajen gina zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa.

Ya jaddada cewa masu tasiri a shafukan sada zumunta sun zama manyan masu yaɗa bayanai a wannan zamani, don haka wajibi ne su riƙa tantance gaskiyar bayanai kafin wallafawa.

«”A yau, saƙon da aka wallafa na iya haifar da fata ko kuma tayar da husuma cikin ɗan lokaci. Don haka bai kamata neman farin jini ko yawan masu kallo ya zama sanadin jefa ƙasa cikin rikici ba,” in ji shi.»

Abdulaziz ya kuma yi kira ga masu amfani da kafafen sada zumunta su taka rawar gani wajen kare zaman lafiyar ƙasa yayin da zaɓen shekarar 2027 ke ƙaratowa, tare da gyara duk wani kuskure idan ya faru.

Ya bayyana cewa a wani ɓangare na shirye-shiryen taron, an horas da sama da mutum 100 daga cikin masu goyon bayan jam’iyyar APC da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan dabarun yaɗa bayanai da kuma bayyana manufofi da nasarorin gwamnati yadda ya kamata.

Haka kuma, ya sanar da ƙaddamar da shirin Gani-Ya-Kori-Ji, wanda zai zagaya jihohin Arewacin Najeriya domin haska ayyukan ci gaba da Gwamnatin Tarayya da gwamnatocin jihohi suka aiwatar, musamman waɗanda ba su samu isasshen haske daga kafafen yaɗa labarai ba.

A cewarsa, taron ya nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kare ‘yancin faɗin albarkacin baki, ƙarfafa tattaunawa da bunƙasa dimokuraɗiyya.

Ya ce an tsara taron ne domin bai wa masu ruwa da tsaki daga sassa daban-daban na Arewacin Najeriya damar tattaunawa kan yadda za a inganta alaƙar gwamnati da jama’a.

A ƙarshe, Abdulaziz ya yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa karɓar baƙuncin taron, yana mai bayyana Kano a matsayin cibiyar siyasa, kasuwanci da tattaunawa a Najeriya.

Ya kuma buƙaci mahalarta taron su fito da shawarwari da sabbin alƙawurra da za su inganta buɗaɗɗen tsarin mulki, ƙarfafa ɗabi’ar aikin jarida da kuma bunƙasa kyakkyawar alaƙa tsakanin gwamnati da al’umma.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gombe Da UNFPA Sun Ƙarfafa Haɗin Gwiwa Don Yaƙi Da Cutar Fistula Da Tamowa
Next Post: Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
Shugaba Saied Yana Cigaba Da Samun Goyon Bayan Al’ummar Kasar Tunisiya Afrika
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
Shugaba Bola Tinubu Ya Saka Hannu A Dokar Zabe Najeriya
Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Kasashen Yamma Suna Cigaba Da Kai Ruwa Rana Akan Nukiliyar Iran Afrika
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kwararru Sun Tabbatar Da Lafiyar Kangimi Dam Bayan Binciken Tsaro Afrika
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
  • Ana Zargin Tsohon Shugaban Kasar Philippines Da Ta’addaci A Lokacin Mulkinsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.