Matar tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Asia El-Rufai, ta yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya tabbatar an yi wa mijinta, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, adalci yayin da yake fuskantar shari’ar da ake yi masa.
Da take magana a ranar Talata a gidan iyalansu da ke Abuja tare da ɗayar matar El-Rufai, Hajiya Aichatou El-Rufai, Asia ta ce ba sa roƙon Shugaban Ƙasa ya tsoma baki a cikin shari’ar, sai dai su tabbatar an mutunta haƙƙoƙin El-Rufai da kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.
Ta tuna irin goyon bayan da ita da mijinta suka bai wa Tinubu a lokacin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023, tana mai cewa sun yi aiki tuƙuru domin samun nasararsa a Jihar Kaduna.
“Mai Girma Shugaban Ƙasa, na yi muku yaƙin neman zaɓe. Na zagaya ko’ina cikin Jihar Kaduna domin neman muku ƙuri’u. Mijina ya tsaya tsayin daka tare da ku. Shin wannan ne sakamakon da iyalinmu suka cancanta?” in ji ta.
Asia ta roƙi Shugaban Ƙasa da ya tabbatar an bai wa El-Rufai damar samun kulawar lafiya, ganawa da lauyoyinsa da kuma iyalansa, tana mai jaddada cewa abin da suke nema shi ne adalci da kuma mutunta doka.
“Ba na roƙon ku ku hana a gurfanar da shi a kotu ba, abin da muke nema shi ne a ba shi haƙƙoƙin ɗan Adam na asali da Kundin Tsarin Mulkin da kuka rantse za ku kare ya tanada,” in ji ta.
Ta kuma yi zargin cewa El-Rufai, wanda ta ce likitoci sun tabbatar yana fama da hawan jini da kuma ciwon sukari, ba ya samun isasshiyar kulawar lafiya yayin da yake tsare.
A cewarta, hana likitansa na kashin kansa, lauyoyinsa da ‘yan uwansa damar ganinsa ya jefa iyalan cikin damuwa matuƙa.
“Mu iyalansa muna cikin firgici. Muna rayuwa cikin fargabar wata rana mu wayi gari da labarin da ba ma fatan ji,” in ji ta.
Asia ta ce ya kamata a bai wa mijinta damar kare kansa yadda ya kamata yayin da shari’arsa ke gudana.
“Ya kamata a ba shi beli cikin sharuddan da suka dace. Idan yana da laifi, kotu ce za ta yanke hukunci. Idan kuma ba shi da laifi, ita ma kotu ce za ta tabbatar da hakan,” ta ƙara da cewa.
Wannan roƙo ya biyo bayan kama likitan El-Rufai, Bello Abubakar, da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka masu Alaƙa (ICPC) ta yi bisa zargin bayar da bayanan da ake zargin ba daidai ba ne game da ziyarar duba lafiyar tsohon gwamnan yayin da yake tsare.


