Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Matar El-Rufai Ta Roƙi Tinubu Ya Tabbatar An Yi Wa Mijinta Adalci
Published: July 8, 2026 at 9:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Matar tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Asia El-Rufai, ta yi kira ga Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da ya tabbatar an yi wa mijinta, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, adalci yayin da yake fuskantar shari’ar da ake yi masa.

Da take magana a ranar Talata a gidan iyalansu da ke Abuja tare da ɗayar matar El-Rufai, Hajiya Aichatou El-Rufai, Asia ta ce ba sa roƙon Shugaban Ƙasa ya tsoma baki a cikin shari’ar, sai dai su tabbatar an mutunta haƙƙoƙin El-Rufai da kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.

Ta tuna irin goyon bayan da ita da mijinta suka bai wa Tinubu a lokacin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2023, tana mai cewa sun yi aiki tuƙuru domin samun nasararsa a Jihar Kaduna.

“Mai Girma Shugaban Ƙasa, na yi muku yaƙin neman zaɓe. Na zagaya ko’ina cikin Jihar Kaduna domin neman muku ƙuri’u. Mijina ya tsaya tsayin daka tare da ku. Shin wannan ne sakamakon da iyalinmu suka cancanta?” in ji ta.

Asia ta roƙi Shugaban Ƙasa da ya tabbatar an bai wa El-Rufai damar samun kulawar lafiya, ganawa da lauyoyinsa da kuma iyalansa, tana mai jaddada cewa abin da suke nema shi ne adalci da kuma mutunta doka.

“Ba na roƙon ku ku hana a gurfanar da shi a kotu ba, abin da muke nema shi ne a ba shi haƙƙoƙin ɗan Adam na asali da Kundin Tsarin Mulkin da kuka rantse za ku kare ya tanada,” in ji ta.

Ta kuma yi zargin cewa El-Rufai, wanda ta ce likitoci sun tabbatar yana fama da hawan jini da kuma ciwon sukari, ba ya samun isasshiyar kulawar lafiya yayin da yake tsare.

A cewarta, hana likitansa na kashin kansa, lauyoyinsa da ‘yan uwansa damar ganinsa ya jefa iyalan cikin damuwa matuƙa.

“Mu iyalansa muna cikin firgici. Muna rayuwa cikin fargabar wata rana mu wayi gari da labarin da ba ma fatan ji,” in ji ta.

Asia ta ce ya kamata a bai wa mijinta damar kare kansa yadda ya kamata yayin da shari’arsa ke gudana.

“Ya kamata a ba shi beli cikin sharuddan da suka dace. Idan yana da laifi, kotu ce za ta yanke hukunci. Idan kuma ba shi da laifi, ita ma kotu ce za ta tabbatar da hakan,” ta ƙara da cewa.

Wannan roƙo ya biyo bayan kama likitan El-Rufai, Bello Abubakar, da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka masu Alaƙa (ICPC) ta yi bisa zargin bayar da bayanan da ake zargin ba daidai ba ne game da ziyarar duba lafiyar tsohon gwamnan yayin da yake tsare.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
Next Post: Gwamnonin Arewa Sun Kaddamar da Kwamitin Asusun Tsaro

Karin Labarai Masu Alaka

Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Sudan Takai Hari Kasar Chadi Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.