Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
Published: July 8, 2026 at 6:41 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mambobin Majami’ar ECWA Gospel da ke kan titin Ashaka a jihar Gombe na ci gaba da tantance irin asarar da suka yi bayan wata gobara ta tashi ta lalata babban zauren cocin.

Gobarar, wadda ta faru a daren Talata, 7 ga Yuli, ta ƙone mimbari, dandalin mawaƙan coci, kayan kiɗa, kayan gudanar da ibada, rufin cikin gini (ceiling), rufin sama da sauran kadarorin cocin.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa bayan an kammala nazarin Littafi Mai Tsarki da misalin ƙarfe 6:00 na yamma, an rufe Majami’ar kamar yadda aka saba.

Sai dai da misalin ƙarfe 8:00 na dare, jami’in tsaron cocin ya hango hayaƙi na tashi daga saman ginin yayin da yake bakin aikinsa. Bayan ya je ya duba, ya tarar da cewa babban zauren cocin ya cika da hayaƙi, lamarin da ya sa ya gaggauta sanar da Faston da ke kula da cocin da kuma sauran mambobin coci.

Nan take mambobin cocin suka hallara domin dakile gobarar kafin ta bazu zuwa sauran sassan ginin.

Mazauna yankin tare da mambobin cocin sun haɗa kai wajen kashe gobarar, yayin da jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Gombe suka isa wurin da manyan motocin kashe gobara guda huɗu, inda daga bisani suka yi nasarar shawo kan gobarar.

Faston da ke kula da Majami’ar, Rabaran Dakta Gideon Danbauchi, ya gode wa Allah da cewa babu wanda ya rasa ransa sakamakon gobarar.

Ya bayyana lamarin a matsayin babban ƙalubale, amma ya ce cocin na da cikakken ƙwarin gwiwa da imani cewa za a sake gina sashen da gobarar ta lalata.

Rabaran Danbauchi ya kuma yaba wa Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Gombe da mazauna yankin saboda gaggawar da suka yi wajen taimakawa domin hana gobarar yaɗuwa.

Ya yi kira ga mambobin cocin, masu fatan alheri da al’ummar Kirista da su ba da gudummawa domin taimakawa wajen gyaran cocin.

Daraktan Fasaha na cocin, Mista Olatunji Daniel, ya ce ya samu labarin gobarar ne bayan ya ga hayaƙi mai yawa yana tashi sama tare da samun kiran gaggawa daga mutanen da ke kusa da cocin.

Ya ce lokacin da ya isa wurin, an riga an kulle cocin, lamarin da ya tilasta wa masu agaji fasa tagogi domin shiga su kashe gobarar, amma ƙarfin wutar ya fi ƙarfinsu.

Ko da yake har yanzu ba a tabbatar da musabbabin gobarar ba, shaidun gani da ido na zargin cewa matsalar wutar lantarki ce ta haddasa tashin gobarar.

Har yanzu ana ci gaba da tantance cikakken girman asarar, amma kiyasin farko ya nuna cewa darajar kayan da gobarar ta lalata na iya haura Naira miliyan 100.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo
Next Post: TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rangadin Ayyukan Tinubu Ya Kai Tawaga Zuwa Kano Northern Bypass Afrika
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.