Majalisar Malaman Yarbawa a Gombe, wato Yoruba Council of Ulama Gombe Nigeria, YCUGN, ta bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Babban Limamin Ƙungiyar Nuruddeen Society of Nigeria, reshen Jihar Gombe.
A cikin saƙon ta’aziyyar da Babban Sakataren majalisar, Sheikh Alfa Okegbemiro Jamiu Okesola, ya sanya wa hannu a ranar 6 ga Satumba, 2026, majalisar ta bayyana marigayin a matsayin uba, malamin addini, shugaba kuma mai koyarwa, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen bautar Allah, yada ilimin addinin Musulunci da kuma haɗa kan al’umma.
Majalisar ta ce marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan Musulmi, tare da bayar da gudunmawa wajen ci gaban ilimin Alƙur’ani da sauran harkokin addini a Jihar Gombe.
A cewar sanarwar, shugabancinsa ya kasance bisa tawali’u, hidima da hikima, inda ya yi amfani da matsayinsa wajen sasanta rikice-rikice, bayar da shawarwari da kuma jagorantar al’umma bisa koyarwar Musulunci.
Majalisar ta kuma bayyana marigayin a matsayin mutum mai karamci da kishin al’umma, musamman talakawa, marayu da ɗaliban ilimin addini.
Ta ce gudunmawar da ya bayar wajen tallafa wa makarantun Islamiyya, masallatai da iyalai a Gombe na daga cikin abubuwan da za su ci gaba da kasancewa cikin tarihin rayuwarsa.
Majalisar Malaman Yarabawa ta yi kira ga mambobin Ƙungiyar Nuruddeen da sauran Musulmi da su ci gaba da riƙe kyawawan ɗabi’un da marigayin ya kasance yana koyarwa, musamman haɗin kai, gaskiya, haƙuri, tawali’u da hidima ga al’umma.
Ta kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da tallafa wa karatun Alƙur’ani da sauran ayyukan da ke inganta rayuwar al’umma da haɗin kan Musulmi.
Majalisar ta yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin, Ya jiƙansa, Ya yalwata masa kabarinsa tare da sanya haske a cikinsa, sannan Ya sanya Aljannar Firdausi ta zama makomarsa.
Haka kuma, majalisar ta roƙi Allah Ya bai wa iyalan marigayin, Ƙungiyar Nuruddeen, al’ummar Yarabawa da ɗaukacin Musulmin Jihar Gombe haƙurin jure wannan babban rashi.
Ta ƙara jaddada buƙatar ci gaba da ayyukan alheri da ilimi da marigayin ya bari, domin su zama abin tunawa da kuma ci gaba da amfanar al’umma.


