Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Majalisar Malaman Yarbawa Ta Yi Jimamin Rasuwar Babban Limamin Nuruddeen A Gombe
Published: September 6, 2026 at 4:45 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: September 6, 2026

Majalisar Malaman Yarbawa a Gombe, wato Yoruba Council of Ulama Gombe Nigeria, YCUGN, ta bayyana alhini da jimami bisa rasuwar Babban Limamin Ƙungiyar Nuruddeen Society of Nigeria, reshen Jihar Gombe.

A cikin saƙon ta’aziyyar da Babban Sakataren majalisar, Sheikh Alfa Okegbemiro Jamiu Okesola, ya sanya wa hannu a ranar 6 ga Satumba, 2026, majalisar ta bayyana marigayin a matsayin uba, malamin addini, shugaba kuma mai koyarwa, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen bautar Allah, yada ilimin addinin Musulunci da kuma haɗa kan al’umma.

Majalisar ta ce marigayin ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan Musulmi, tare da bayar da gudunmawa wajen ci gaban ilimin Alƙur’ani da sauran harkokin addini a Jihar Gombe.

A cewar sanarwar, shugabancinsa ya kasance bisa tawali’u, hidima da hikima, inda ya yi amfani da matsayinsa wajen sasanta rikice-rikice, bayar da shawarwari da kuma jagorantar al’umma bisa koyarwar Musulunci.

Majalisar ta kuma bayyana marigayin a matsayin mutum mai karamci da kishin al’umma, musamman talakawa, marayu da ɗaliban ilimin addini.

Ta ce gudunmawar da ya bayar wajen tallafa wa makarantun Islamiyya, masallatai da iyalai a Gombe na daga cikin abubuwan da za su ci gaba da kasancewa cikin tarihin rayuwarsa.

Majalisar Malaman Yarabawa ta yi kira ga mambobin Ƙungiyar Nuruddeen da sauran Musulmi da su ci gaba da riƙe kyawawan ɗabi’un da marigayin ya kasance yana koyarwa, musamman haɗin kai, gaskiya, haƙuri, tawali’u da hidima ga al’umma.

Ta kuma buƙaci al’umma da su ci gaba da tallafa wa karatun Alƙur’ani da sauran ayyukan da ke inganta rayuwar al’umma da haɗin kan Musulmi.

Majalisar ta yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin, Ya jiƙansa, Ya yalwata masa kabarinsa tare da sanya haske a cikinsa, sannan Ya sanya Aljannar Firdausi ta zama makomarsa.

Haka kuma, majalisar ta roƙi Allah Ya bai wa iyalan marigayin, Ƙungiyar Nuruddeen, al’ummar Yarabawa da ɗaukacin Musulmin Jihar Gombe haƙurin jure wannan babban rashi.

Ta ƙara jaddada buƙatar ci gaba da ayyukan alheri da ilimi da marigayin ya bari, domin su zama abin tunawa da kuma ci gaba da amfanar al’umma.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Sanda Sun Haramta Amfani Da Drones Ba Tare Da Izinin NCAA Ba
Next Post: Hukumar Ruwa Ta Gombe Ta Horas Da Ma’aikatan Sashen Kasuwanci Kan Ka’idojin Aiki

Karin Labarai Masu Alaka

Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Somaliya: Ba Za Mu Dauki Wulakancin Donald Trump Ba! Sauran Duniya
  • Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
  • Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.