Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno
Published: July 12, 2026 at 2:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya rabawa mambobin masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke aiki a ƙananan hukumomin Bayo da Hawul tallafin kuɗi da ya kai jimillar naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m), a wani mataki na ƙarfafa musu gwiwa.

A ƙaramar hukumar Bayo, Gwamna Zulum ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 29 kuɗi naira dubu hamsin (N50,000). Haka kuma, ya bai wa Corps Liaison Officer (CLO) da Local Government Inspector (LGI) naira dubu ɗari (N100,000) kowannensu. Jimillar kuɗin da aka rabawa a ƙaramar hukumar ta Bayo ta kai naira miliyan 1 da dubu 650 (N1.65m).

A ƙaramar hukumar Hawul kuwa, Gwamnan ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 125 naira dubu hamsin (N50,000), yayin da Corps Liaison Officer (CLO) ya karɓi naira dubu ɗari (N100,000), sannan Local Government Inspector (LGI) ya karɓi naira dubu ɗari biyu (N200,000). Jimillar kuɗin da aka raba a Hawul ta kai naira miliyan 6 da dubu 550 (N6.55m).

Gaba ɗaya, ƙananan hukumomin Bayo da Hawul sun amfana da tallafin da ya kai naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m).
Da yake tsokaci kan wannan tallafi, Kodinetan Hukumar NYSC na jihar Borno, Malam Nasir Bello, ya bayyana jin daɗinsa, yana mai cewa wannan karamci bai zo masa da mamaki ba, domin ya zama al’adar Gwamna Zulum na kula da jin daɗin mambobin NYSC.

Ya ƙara da cewa, ci gaba da ba da muhimmanci ga walwala da jin daɗin mambobin NYSC a jihar Borno zai ƙara jawo hankalin matasa masu yi wa ƙasa hidima su karɓi aiki a jihar cikin kwarin gwiwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci
Next Post: An Yaba Wa Gwamnatin Bauchi Bisa Karban Bakuncin Gasar Polo

Karin Labarai Masu Alaka

Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika
  • Gwamna Inuwa Yahaya Ya Bukaci Al’ummar Gombe Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Ta’addanci Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Murtala Garo Murnar Zama Mataimakin Gwamnan Kano Labarai
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Jamhuriyar Congo Zata Cigaba Da Fitar Da Ma’adanai Afrika
  • Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.