Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya rabawa mambobin masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke aiki a ƙananan hukumomin Bayo da Hawul tallafin kuɗi da ya kai jimillar naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m), a wani mataki na ƙarfafa musu gwiwa.
A ƙaramar hukumar Bayo, Gwamna Zulum ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 29 kuɗi naira dubu hamsin (N50,000). Haka kuma, ya bai wa Corps Liaison Officer (CLO) da Local Government Inspector (LGI) naira dubu ɗari (N100,000) kowannensu. Jimillar kuɗin da aka rabawa a ƙaramar hukumar ta Bayo ta kai naira miliyan 1 da dubu 650 (N1.65m).

A ƙaramar hukumar Hawul kuwa, Gwamnan ya bai wa kowane ɗaya daga cikin mambobin NYSC 125 naira dubu hamsin (N50,000), yayin da Corps Liaison Officer (CLO) ya karɓi naira dubu ɗari (N100,000), sannan Local Government Inspector (LGI) ya karɓi naira dubu ɗari biyu (N200,000). Jimillar kuɗin da aka raba a Hawul ta kai naira miliyan 6 da dubu 550 (N6.55m).
Gaba ɗaya, ƙananan hukumomin Bayo da Hawul sun amfana da tallafin da ya kai naira miliyan 8 da dubu 200 (N8.2m).
Da yake tsokaci kan wannan tallafi, Kodinetan Hukumar NYSC na jihar Borno, Malam Nasir Bello, ya bayyana jin daɗinsa, yana mai cewa wannan karamci bai zo masa da mamaki ba, domin ya zama al’adar Gwamna Zulum na kula da jin daɗin mambobin NYSC.
Ya ƙara da cewa, ci gaba da ba da muhimmanci ga walwala da jin daɗin mambobin NYSC a jihar Borno zai ƙara jawo hankalin matasa masu yi wa ƙasa hidima su karɓi aiki a jihar cikin kwarin gwiwa.


