Daga Zainab Babaji a Jos Najeriya
Dakarun rundunar wanzar da zaman lafiya ta Operation ENDURING PEACE’ sun yi nasarar cafke wassu batagari shida da ke safarar makamai da take zargin suna kai wa ‘yan ta’adda ne.
Jami’an dake aiki a kauyen Samaru da ke gundumar Zonkwa a karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna, sun cimma nasarar ne yayin da suke gudanar da aiki a shingen binciken ababan hawa na Samaru.
Sanarwa daga kakakin rundunar Operation Enduring Peace, Cinonso Polycarp Oteh yace wadanda aka cafken sun amsa cewa suna kan hayar zuwa jihar Neja ne daga garin Jos na jihar Filato.
Sanarwar tace nasarar chapke mutanen da aka yi da misalin karfe 09:40 na safiyar litinin 13 ga watan yuli 2026, wani bangare ne na ci gaba a yunkurin dakile ayyukan ta’addanci da Operation ENDURING PEACE ke gudanarwa a yankin.
Sanarwar ta kara da cewa a yayin samamen da ya kai ga nasarar cafke mutanen a cikin mota mai launin toka da lambar EDO GUE-722-LV.
Makaman da jami’an suka kwato sun hada da bindigogi kirar AK 47 guda 3 da kananan bindigogi guda 4 da wata mota kirar Marsandi kuma ana kan gudanar bincike.

Operation ENDURING PEACE ta yabawa jama’a bisa hadin kai da ci gaba da ba ta goyon baya tare da bukatar su da su ci gaba da lura da yankunan su tare da kai rahoton mutanen da suke zargi ga hukumomin tsaro da suka dace.


