Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci
Published: July 18, 2026 at 5:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe a Najeriya ta karɓi bakuncin Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda mai kula da shiyya ta 12 (Zone 12), AIG Vungmoh S. M. Kwaimo, a wata ziyarar aiki da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa tare da zaburar da jami’an ‘yan sanda su ƙara himma wajen yaƙi da aikata laifuka da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.

Taron, wanda ya gudana a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe, ya haɗa manyan jami’an ‘yan sanda daga sassa daban-daban na jihar da kuma mambobin Kwamitin Hulɗa Tsakanin ‘Yan Sanda da Al’umma (PPRC).

An gudanar da laccoci da tattaunawa domin ƙara ƙwarewar aiki, inganta ayyukan jami’an tsaro da kuma ƙarfafa matakan tabbatar da tsaro a yankin.

A jawabinsa na maraba, Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Ahmed Umar Chuso, ya gode wa AIG Kwaimo bisa ziyarar tare da sake jaddada cikakken biyayya da ƙudirin rundunar na ci gaba da gudanar da aikinta bisa manufofin Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya.

CP Chuso ya bayyana irin nasarorin da rundunar ta samu wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar Gombe, yana mai cewa ci gaba da tattaunawa da jami’ai da ƙarfafa haɗin gwiwa na taka muhimmiyar rawa wajen ɗaga ƙwarin gwiwa, tabbatar da ladabtarwa da kuma inganta gudanar da ayyukan da kundin tsarin mulki ya ɗora wa rundunar.

A nasa jawabin, Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, AIG Vungmoh Kwaimo, ya bayyana gamsuwarsa da yadda Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ke gudanar da ayyukanta ƙarƙashin jagorancin CP Ahmed Umar Chuso.

Ya yaba da nasarorin da rundunar ta samu da kuma zaman lafiyar da ake morewa a jihar, tare da ƙarfafa jami’ai da su ci gaba da jajircewa domin dorewar waɗannan nasarori.

AIG Kwaimo ya bayyana cewa ziyarar ta Gombe ta biyo bayan irin wannan rangadin duba ayyukan runduna da ya gudanar a Jihar Bauchi.

Ya ce manufar rangadin ita ce tantance yadda ake gudanar da ayyukan ‘yan sanda a dukkan jihohin da ke ƙarƙashin Zone 12, sauraron ƙalubalen jami’ai da kuma samar da mafita ta hanyar tattaunawa mai ma’ana domin ƙara inganta ayyukan tsaro da ci gaba da aiwatar da manufar rundunar ta rashin sassauci ga masu aikata laifuka da ta’addanci.

Haka kuma, AIG Kwaimo ya yabawa Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, IGP Olatunji Rilwan Disu, bisa ƙoƙarin da yake yi wajen inganta jin daɗin jami’an rundunar.

Ya ce sauye-sauyen da IGP ya kawo sun fara haifar da sakamako mai kyau, sannan ya buƙaci jami’an da su rama wannan kulawa ta hanyar nuna cikakken biyayya, jajircewa, ƙwarewa a aiki da kuma yi wa ƙasa hidima ba tare da son kai ba.

Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Ƙungiyar Mata Sunyi Kira Ga Jam’iyar P R P Da Ta Dauki Baheejja A Matsayin Mataimakiyar Gwamnan A Bauchi 2027
Next Post: Mamakon Ruwan Sama Da Iska Ya Hallaka Mutane Uku A Jihar Yobe

Karin Labarai Masu Alaka

Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
Pakistan Zata Karbi Bakwancin Saudiya, Turkiyya Da Masar Afrika
Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Amurka Tasakawa Sojin Rwanda Takunkumi Afrika
  • ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.