Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS
Published: July 21, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da ta ɗauki tsauraran matakai kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi da ake kai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka a ƙasar Afirka ta Kudu.

Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yayin taron shugabannin ECOWAS karo na 69 da aka gudanar a birnin Freetown na ƙasar Saliyo.

Ya ce ya zama dole ECOWAS ta gabatar da batun a gaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), domin a ɗauki matakin gaggawa kan hare-haren da ke barazana ga rayuka da dukiyoyin ‘yan Afirka.

Shugaban ya ce gwamnatin Najeriya ta yi Allah wadai da hare-haren, tana mai bayyana cewa ci gaba da yin shiru ta fuskar diflomasiyya kan irin waɗannan abubuwa na iya ƙarfafa masu aikata su.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta kwashe sama da ‘yan Najeriya 1,490 daga Afirka ta Kudu ta hanyar jigilar jirage bakwai domin kare rayukansu sakamakon rikice-rikicen.

Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na tattaunawa da Ghana domin haɗa kai wajen matsa wa Tarayyar Afirka lamba ta ɗauki matakin hukunta Afirka ta Kudu kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi.

An bayyana cewa hare-haren ba ‘yan Najeriya kaɗai suka shafa ba, har ma da dubban ‘yan wasu ƙasashen Afirka da ke zaune da aiki a Afirka ta Kudu.

A wani ɓangaren kuma, Shugaba Tinubu ya sake jaddada aniyar Najeriya na goyon bayan shirin ECOWAS Compact for the Future of Regional Integration, wanda ke da nufin ƙarfafa haɗin kan ƙasashen yankin, inganta shugabanci nagari, bunƙasa kasuwanci tsakanin ƙasashe, da samar da kasuwar hada-hadar yanar gizo guda ɗaya domin faɗaɗa damar ayyukan yi ga matasa.

Ya ce tabbatar da shugabanci nagari da kare rayuka da haƙƙin ‘yan Afirka su ne manyan ginshiƙan samar da zaman lafiya da ci gaban nahiyar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shari’ar Ta’addanci: Manyan Jagororin Ansaru Biyu Sun Amsa Laifi A Abuja
Next Post: Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Kawo Ƙarshen Aikin Kwamitin Sayar Da Kaddarorin Gwamnati Afrika
Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
Mutane 27 Sun Rasa Rayukan Su A Najeriya Afrika
Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
  • Sanarwar MDD Ya Nuna Aniyar Mayakan RSF Na Kisan Kare Dangi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Maso Yammacin Najeriya Sun Halarci Taron Inganta Makashi A Birnin Landan Afrika
  • Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.