Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Published: November 30, 2025 at 3:34 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Mataimakin Shugaban jami’ar jihar Gombe Ferfesa Sani Yauta ya kaddamar da littafi mai take Sauye-Sauye a bangaren ilimi da shugabanci.

Jami’ar Gombe (GSU) ta gudanar da bikin kaddamar da sabon littafi mai suna “Dynamics of Educational Administration and Planning” wanda Farfesa Sani Ahmed Yauta ya rubuta, a dakin taro na Haruna Kadir Rasheed dake jami’ar.

Taron ya sami halartar jami’an gwamnati, malamai, da baki na musamman.

Shugaban taron, mataimakin Gwamnan Jihar Gombe, Dr. Manassah Daniel Jatau, ya yabawa Farfesa Yauta bisa wannan gudummawar ilimi da ya bayar a sashin ilimi.

Fitattun jami’an gwamnati sun halarci bikin, ciki har da shugaban ma’aikata na jihar Gombe, Alhaji Ahmed Kasimu Abdullahi, Shugaban Jami’ar Tarayya dake Kashere, Farfesa Umaru Pate, Shugaban Jami’ar Lincoln University, Farfesa Adamu Sadiq Abubakar da Shugabar kwalejin koyon jinya, tare da wasu shugabannin cibiyoyi a jihar.

Haka zalika, Daraktan Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH), Farfesa Yusuf Muhammed Abdullahi, ya hallarci bikin tare da sauran manyan baki.

A jawabin sa, Babban Mai Kaddamarwa, Arc. Yunusa Yakubu, ya jinjina wa Farfesa Yauta kan jajircewarsa wajen bunkasa ilimi, yana mai bayyana littafin a matsayin abin dogaro ga masu gudanarwa, masu bincike da masu tsara manufofin ilimi.

Littafin dai wata dama ce da mahukunta zasu iya amfani da ita don sabutan tsari da manhajoji da ake amfani da su a makarantu a kasar baki daya. An kuma ja hankalin sauran malamai a fannin ilimi da su bada irin wadannan gudumawar don habaka ilimi, da ganin an samar da yanayi wanda ilimi a kasar zai yi gogayya da kasashe masu cigaba a fanin ilimi.

Kabatar da kasidu da taron karawa juna sani irin wadannan na da matukara muhimanci ga cigaban ilimi, ta haka ma ana iya sako daliban ilimi wajen shirya irin wadannan tarukan, da muna musu makamar aiki; a cewar daya daga cikin mahalarta taron.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025
Next Post: Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi

Karin Labarai Masu Alaka

Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci Labarai
Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya
Tinubu Zai Gabatar Da Jawabi ga Shugabannin Duniya A Taron UNGA Afrika
Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Kasar Da Soke Shari’a A Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
  • Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • Gombe Ta Ƙaddamar da Allurar Rigakafin HIV Ta LEN PrEP Afrika
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.