Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa
Published: December 1, 2025 at 5:12 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 1, 2025

Dr. Usman Isiyaku, mai sharhi akan al’ammuran yau da kullum, shugabanci na gari, ya ayyana wasu kadan daga cikin tsare-tsaren na gwamnatin Tinubu, a kan al’ammurra da suka shafi jagorancin Najeriya.

Inda yake cewa “Bisa ga al’adar gwamnatin Bola Ahmad Tinubu, ba wani abun mamaki bane ko sabon abu, don ya nada Yarbawa, a mafi akasari da mukamai masu girma. Idan aka duba za’a ga cewar tun fara mulkin shi da irin wannan salon ya fara.”

A wasu lokutta kuwa akan ga cewar Arewa tana da girma, don haka idan aka bata wasu tsirarun mukamai sai aga kamar an yi mata wata hikima. Sau da yawa ‘yan Arewa dake tare da gwamnatin ta shi, basu da wani karfi da za su iya gaya mishi gaskiya. Mafi akasari ma ‘yan abi yarima ne a sha kida.

Don kuwa da yawa daga cikin su, ba wai tunanin kasar ne a zukatan su ba, mafi akasari son kansu da nasu ne a zukatansu. Bugu da kari, duk wani abu da za’a gani a wannan gwamnatin, to yana da alaka da gwamnatin da ta gabata, ta Margayi Muhammadu Buhari.

Tsari ne da ba’a la’akari da cancanta wajen zabo wadanda zasu wakilci kasa, ko jama’a. Don haka ba wani abun mamaki bane don anga nadin jakadu na bangaren Yarbawa da basu da kwatankwacin kashi 10 na adadin yawan mutan Arewa, amma suke da jakadu 11 kana aka kai su kasashe manya a duniya.

Inda ita kuma Arewa ta tashi da jakadu 5 daga bangaren Arewa maso yamma, sai 5 daga Arewa maso gabas, kana wasu 5 da ke wakiltar Arewa ta tsakiya. Abun ala’akari a nan shine, yawan mutane da suka fito daga Arewa maso yamma da ke da jihohi 7, sun fi yawan mutane da suka fito daga baki daya Kudu maso Yamma da aka basu jakadu 11.

Haka kuma, wannan gwamnati ce da take la’akari da mutane da suka wahalar mata koda kuwa basu cancanta, da kuma mutane da suka fito daga bangare daya, ko kuwa bangaranci na addini, da na kabilanci, wanda ta haka ne zai ba mutum damar samu wani babban matsayi, ba la’akari da irin gudunmawar da zaka bada ake yi ba.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano
Next Post: Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi”

Karin Labarai Masu Alaka

Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.