Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

IMC Kaduna Ta Buƙaci Jama’a Su Fifita Haɗin Kai Da Zaman Lafiya
Published: September 8, 2026 at 8:18 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Cibiyar Sasanta Rikice-rikicen Addinai (IMC) Kaduna, tare da haɗin gwiwar Network of Peace Journalism, Rigar Yanchi, Community Peace Observers (CPOs), Kaduna Peace Justice Forum, da Conflict Mitigation and Management Regional Council (CMMRC), ta bayyana matuƙar damuwarta kan musayar kalamai, sharhin kafafen yaɗa labarai da kuma muhawarar jama’a da suka biyo bayan kalaman Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), da kuma tsoffin korafe-korafe da suka shafi gwamnatin tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai.

Ƙungiyoyin sun ce, duk da cewa muhawara mai ƙarfi ta dimokuraɗiyya, ‘yancin faɗar albarkacin baki da kuma bayyana ra’ayoyi kan tarihi da harkokin mulki muhimman ginshiƙai ne na dimokuraɗiyya mai tasowa, ya kamata a yi taka-tsantsan domin muhawarar siyasa tsakanin manyan jami’an gwamnati na iya sake tayar da rarrabuwar kawuna ta ƙabilanci, addini da bangaranci a cikin al’ummar da har yanzu ke da rauni wajen zaman lafiya.

Sun ce jihar Kaduna ta biya babban farashi sakamakon rarrabuwar kawuna da aka samu a baya, don haka ya kamata a karkata dukkan ƙoƙari wajen warkar da raunukan baya, sulhu da samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

A saboda haka, ƙungiyoyin sun yi kira cikin gaggawa ga al’ummar jihar Kaduna, Arewacin Najeriya da ma ƙasar baki ɗaya da su ƙi rarrabuwa tare da fifita mutuntaka da haɗin kai.

Sun buƙaci jama’a daga kowane ƙabila, addini da yanki da kada su bari kalaman siyasa ko rashin jituwar shugabanni su koma sanadin ƙiyayya da rikici a tsakanin al’umma.

Sun ce burin da ya haɗa kowa, wanda ya haɗa da zaman lafiya, tsaro da bunƙasar tattalin arziki, ya fi duk wani bambancin siyasa ko na kashin kai muhimmanci.

Ƙungiyoyin sun kuma yi kira da a rungumi tattaunawa mai ma’ana, shugabanci na gaskiya da kuma ɗaukar nauyin zama ɗan ƙasa nagari, ta hanyar magance tsoffin korafe-korafe ta hanyoyin da hukumomi suka tanada, da nuna tausayi da fahimtar juna, maimakon amfani da bambance-bambancen al’umma wajen cimma manufofin siyasa.

Sun kuma yi kira ga shugabannin al’umma, matasa da shugabannin addinai da su yi taka-tsantsan, tare da jagorantar tattaunawar jama’a zuwa ga fahimtar juna da zaman lafiya.

Ƙungiyoyin sun yaba da matakan da gwamnatin yanzu karkashin Gwamna Uba Sani, da kuma wasu ƙungiyoyi da daidaikun mutane, ke ɗauka domin inganta haɗin kai, cike tsoffin gibin da ke tsakanin al’umma da kuma dawo da amincewar jama’a ga harkokin gwamnati.

Sun ƙarfafa dukkan masu ruwa da tsaki da su ƙara mara wa hanyoyin samar da zaman lafiya a matakin al’umma, tsarin Gargaɗin Farko da Amsa da Wuri (EWER), da shirye-shiryen haɗin kan mabiya addinai baya, domin ƙarfafa zaman tare da haɗin kan al’umma.

A wani kira da suka yi ga shugabannin ƙasa da jihohi, ƙungiyoyin sun tunatar da ’yan siyasa, shugabannin addinai, dattawan ƙasa da sauran fitattun mutane cewa kalaman shugabanni na da matuƙar tasiri a cikin al’ummar da ta ƙunshi ƙabilu da addinai daban-daban, musamman a Kaduna da Najeriya baki ɗaya.

Sun bukaci shugabanni a dukkan matakai da su zama abin koyi wajen haɗa kan jama’a, su rage kalaman da ka iya haifar da tashin hankali, tare da mai da hankali kan haɗin gwiwa wajen gina ƙasa.

Sun jaddada cewa Jihar Kaduna gida ce ga dukkan al’ummominta na asali, daga Arewa zuwa Kudu, Gabas zuwa Yamma.

Sun ce ƙarfin Kaduna a koyaushe yana cikin bambancin al’ummarta, juriyarta da kuma ƙarfinta na zaman tare a matsayin al’umma ɗaya.

“Ba za mu bari rikice-rikicen siyasar jiya su raba mu ba. Tare za mu ci gaba da gina Kaduna mai zaman lafiya, wadata da haɗin kai, da kuma Najeriya mafi ƙarfi,” in ji ƙungiyoyin.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamna Namadi Ya Amince Da Naɗin Sabon Sarkin Gumel
Next Post: Yara Miliyan 16 Sun Amfana Da Azithromycin A Karkashin Shirin SARMAAN

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
An Samu Bullar Cutar COVID 19 A Najeriya Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • An Gabatar Da Sabbin Kudurorin Kare Muhalli Da Gandun Daji A Gombe Afrika
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Game Da Matsalar Tsaro A Najeriya Najeriya
  • Kano: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Amince da Garo A Matsayin Mataimakinsa Na 2027 Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Dawo Da Kudaden Ma’aikata Afrika
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.