Gwamnan jihar Gombe kuma Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, NNGF, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi kira da a kara hadin gwiwa tsakanin gwamnati, masana ilimi da malaman addinin Musulunci mata, domin samar da hanyoyin magance manyan kalubalen da ke addabar Arewacin Najeriya.
Gwamnan ya yi wannan kiran ne a yayin wasu taruka daban-daban da ya gudanar da manyan malaman jami’o’i da kuma Ulaman mata daga sassan Arewacin Najeriya a Abuja.
Taron da Ofishin Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Siyasa da Sauran Batutuwa, Honarabul Ibrahim Kabir Masari, ya shirya, ya gudana ne karkashin taken “Consolidating the Renewed Hope Agenda: President Bola Ahmed Tinubu’s Achievements and the Road to 2027.”
Taron ya hada daruruwan masana ilimi da Ulaman mata, domin tattauna matsalolin tsaro, yawan yara da ba sa zuwa makaranta, samar da abinci, ilimin sana’o’i, zaman lafiya da kuma rikicin manoma da makiyaya.
Gwamna Inuwa, wanda kuma shi ne Sakataren Renewed Hope Ambassadors, ya ce Arewacin Najeriya ba zai iya shawo kan kalubalen da yake fuskanta ba tare da amfani da ilimi, kwarewa da binciken masana ba.
Ya bukaci masana da su yi amfani da iliminsu da bincikensu wajen samar da dabarun magance matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta, tare da kara mai da hankali kan ilimin sana’o’i domin bai wa matasa dabarun dogaro da kai.
Dangane da rikicin manoma da makiyaya, Gwamnan ya jaddada muhimmancin zaman lafiya da fahimtar juna, yana mai cewa kafa Ma’aikatar Raya Kiwo ta musamman da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi wata muhimmiyar manufa ce da za ta iya taimakawa wajen sauya fasalin bangaren kiwo da magance rikicin manoma da makiyaya.
Gwamna Inuwa ya kuma yaba wa Ulaman mata kan gudunmawar da suke bayarwa wajen inganta tarbiyyar iyali, zaman lafiya da hadin kan al’umma.
Ya ce mata malaman addinin Musulunci na da muhimmiyar rawa wajen karfafa zaman lafiya, tarbiyyar yara, kyawawan dabi’u da zaman tare a tsakanin al’umma.
Gwamnan ya tabbatar wa mahalarta tarukan cewa irin wannan tuntuba za ta ci gaba, tare da fadada ta zuwa sauran jihohin Arewacin Najeriya domin karfafa fahimtar juna da samar da hanyoyin aiwatar da manufofin gwamnati yadda ya kamata.
A nasa jawabin, mai shirya tarukan kuma Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Siyasa da Sauran Batutuwa, Honarabul Ibrahim Kabir Masari, ya ce an shirya tarukan ne domin samar da ingantacciyar hanya da gwamnati za ta rika tuntubar masana da sauran masu ruwa da tsaki kan harkokin kasa.
Ya ce tuntubar masana ba wai don siyasa kadai ba ne, illa dai domin amfani da ilimi, kwarewa da bincike wajen nemo mafita ga matsalolin da kasar ke fuskanta.
A karshen tarukan biyu, mahalarta sun gabatar da takardun matsaya, wadanda suka kunshi shawarwari da kudurorin da aka cimma.


