Gwamnatin jihar Gombe ta fara wani shirin rigakafin cutar diphtheria na gaggawa, bayan da aka samu rahoton mutane kusan 332 da suka kamu da cutar a ƙananan hukumomi huɗu na jihar.
Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Akko, Gombe, Kwami da Funakaye.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Gombe ta umarci shugabannin makarantu a faɗin jihar da su ba jami’an lafiya cikakken haɗin kai yayin gudanar da aikin rigakafin.
A cewar umarnin ma’aikatar, kashi na farko na aikin rigakafin zai gudana daga ranar 20 zuwa 24 ga watan Satumba na shekarar 2026.
Ma’aikatar ta bayyana cewa za a yi wa yara kashi na biyu na rigakafin kwanaki 14 bayan an yi na farko, yayin da za a gudanar da kashi na uku kuma na ƙarshe bayan kwanaki bakwai.
An kuma umarci shugabannin makarantu da su wayar da kan ɗalibai, iyaye, ƙungiyoyin iyaye da malamai (PTA), da kwamitocin kula da makarantu (SBMC) game da muhimmancin aikin rigakafin.
Haka kuma, an buƙaci makarantu su bai wa jami’an lafiya da aka amince da su damar shiga wajen ɗalibai domin gudanar da rigakafin.
Ma’aikatar ta kuma yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su tallafa wa matakan da ake ɗauka domin dakile yaɗuwar cutar a jihar.
Cutar diphtheria cuta ce mai saurin yaɗuwa wadda kwayar cuta ke haifarwa, kuma galibi tana shafar hanyoyin numfashi na sama. Ana iya yaɗa ta ta hanyar ɗigon ruwa daga numfashin mutum mai ɗauke da cutar ko kuma ta hanyar kusanci da wanda ya kamu da ita.
Barkewar cutar ta sa hukumomi ƙara kaimi wajen gudanar da rigakafi da wayar da kan jama’a, musamman a makarantu da al’ummomin da ke cikin ƙananan hukumomin da abin ya shafa.
Hukumomin lafiya na ci gaba da kira ga jama’a da su ba jami’an rigakafi haɗin kai domin taimakawa wajen dakile yaɗuwar cutar da kare lafiyar al’umma.


