Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a
Published: December 3, 2025 at 5:57 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Shugabannin Fulani a Jihar Nejan Nigeria sun koka akan yadda suka ce Jami’an Tsaron ‘Yan-banga na cin zarafin Fulanin ba tare da tantance mai laifi ko mara laifi.

Wannan dai yana zuwa ne bayan da aka yi zargin wasu ‘yan bindiga a yankin karamar Hukumar Mashegu sun ci zarafin shugaban kungiyar makiyaya ta Miyatti Allah tare da wasu Fulanin su 13.
Bayanai dai sun nuna cewa ‘yan bangan sun yima wadan nan Fulani daurin goro tare da gana musu azaba da a yanzu haka suna karbar magani a babbar Asibitin Gwamnati dake Kontagora,
Alh. Muhammadu Mabbe, shine shugaban Fulanin na karamar Hukumar Magama da ya shiga hannun wadan nan ‘Yan banga da a yanzu haka yake kwance cikin wani mawuyancin hali, yace ‘yan bangar sun sameshi a kofar gidan Sarkin koso ne a dai dai lokacin da suke kokarin jana’izar wani yaron su da aka kashe.
Shugaban Babban Jami’i a Ma’aikatar Kula da Harkokin Makiyaya ta Jihar Neja Malam Ababakar Kamfanin Bobi yayi karin haske akan irin azabar da aka basu.
Sarkin Fulanin Minna Alhaji Hasan Shiroro, wanda shima a kwanakin baya yace ‘yan bangar sun bindige yaro kuma nan take ya mutu har lahira.
Mun tuntubi shugaban ‘yan bangar na Jihar Neja Nasiru Muhwmmad Manta, yace basu da hannu a ciki, amma kuma zasu gudanar da bincike akan lamarin.
Tini dai masu kare hakkin dan adam suka bayyana damuwa akan wannan lamari Kwamrade Kabiru Idris Jami’i ne a hukumar kare hakkin dan adam ne a Jihar Nejan, inda yace basu yadda da wannan cin zarafin ba.
Suma masana a fannin tsaron da zamantakewa suka nuna bukatar dakatar da irin wannan daukar doka a hannu, don shawo kan matsalolin tsaro da Najeriya ke fama dashi.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu
Next Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun Labarai
Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Nnamdi Kanu Zai Daukaka Kara Har Zuwa Kotun Koli Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari Afrika
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
  • Haɗin Gwiwar GOSERC Da Savannah Zai Ƙarfafa Rarraba Wutar Lantarki A Faɗin Jihar Gombe Afrika
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.