Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi
Published: November 30, 2025 at 7:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Zamu tabbatar da kawo karshen hadura a lokacin Bukukuwan karshen shekara – inji Jami’an Hukumar kiyaye hadura a Gombe.

Hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jihar Gombe ta shirya taron fadakar da jama’a game da illar gudu fiye da kima, tare da tukin ganganci yayin bukukuwan karshen shekara.

Kwamandan hukumar kiyaye hadura a jihar Gombe, Mr Samson Kaura ne ya bayyana haka lokacin jawabi ga direbobi da sauran jama’a, yayin gangamin a dakin taro na tashar Dankwanbo Mega Park dake Gombe.

Mr. Kaura, ya tabbatar da cewa ana samun yawan tafiye tafiye a karshen shekara, a saboda haka yabukaci masu ababen hawa da su rika lura tare da bin ka’idojin hanya domin kare rayuwar al’umma.

Ya tabbatar da cewa, ansamu hadura fiye da arba’in da shida a tsakiyar wannan shekarar, kuma mutane sha bakwai sun mutu a jihar Gombe.

A jawaban su, shugaban riko na tashar Dankwanbo Mega Park Malam Sani Sabo da shugaban kungiyar ‘yan achaba a jihar Gombe, Malam Kabiru Jafaru sun bukaci gwamnati da tayi la’akari da gyara hanyoyi da suka lalace a jihar domin gujewa samun hadura.

Malam Sani Sabo da Kabiru Jafaru, sun lissafo hanyar Gombe zuwa Dukku zuwa Darazo, hanyar Gombe zuwa Biu zuwa Maiduguri da hanyar Gombe zuwa Bauchi a matsayin hanyoyi masu muni. Wanda kuma suna haifar da hadura saboda lalacewar su, Inda su kayi fatan gwamnati zata kawo karshen wannan wahalhalu da jama’a ke fuskanta.

A nasu bangaren, daraktar hukumar wayar da kan al’umma jihar Gombe Miss Adalin Waye Patari, shugaban Direbobi na NURTW Malam Musa Yunusa da hakimin Kagarawal Alhaji Usman Ali sun bukaci Direbobi dasu gujewa shaye-shaye a yayin tuki, tare da yawaita gudu fiye da kima.

Inda suka tabbatar da cigaba da fadakar da mambobin su da jama’ar gari domin gujewa samun hadura a fadin kasar nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Next Post: Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
  • Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
  • Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • Ana Sa Ran FIFA Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Najeriya Ta Shigar Kan DR Congo Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.