Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi
Published: November 30, 2025 at 7:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Zamu tabbatar da kawo karshen hadura a lokacin Bukukuwan karshen shekara – inji Jami’an Hukumar kiyaye hadura a Gombe.

Hukumar kiyaye hadura ta kasa reshen jihar Gombe ta shirya taron fadakar da jama’a game da illar gudu fiye da kima, tare da tukin ganganci yayin bukukuwan karshen shekara.

Kwamandan hukumar kiyaye hadura a jihar Gombe, Mr Samson Kaura ne ya bayyana haka lokacin jawabi ga direbobi da sauran jama’a, yayin gangamin a dakin taro na tashar Dankwanbo Mega Park dake Gombe.

Mr. Kaura, ya tabbatar da cewa ana samun yawan tafiye tafiye a karshen shekara, a saboda haka yabukaci masu ababen hawa da su rika lura tare da bin ka’idojin hanya domin kare rayuwar al’umma.

Ya tabbatar da cewa, ansamu hadura fiye da arba’in da shida a tsakiyar wannan shekarar, kuma mutane sha bakwai sun mutu a jihar Gombe.

A jawaban su, shugaban riko na tashar Dankwanbo Mega Park Malam Sani Sabo da shugaban kungiyar ‘yan achaba a jihar Gombe, Malam Kabiru Jafaru sun bukaci gwamnati da tayi la’akari da gyara hanyoyi da suka lalace a jihar domin gujewa samun hadura.

Malam Sani Sabo da Kabiru Jafaru, sun lissafo hanyar Gombe zuwa Dukku zuwa Darazo, hanyar Gombe zuwa Biu zuwa Maiduguri da hanyar Gombe zuwa Bauchi a matsayin hanyoyi masu muni. Wanda kuma suna haifar da hadura saboda lalacewar su, Inda su kayi fatan gwamnati zata kawo karshen wannan wahalhalu da jama’a ke fuskanta.

A nasu bangaren, daraktar hukumar wayar da kan al’umma jihar Gombe Miss Adalin Waye Patari, shugaban Direbobi na NURTW Malam Musa Yunusa da hakimin Kagarawal Alhaji Usman Ali sun bukaci Direbobi dasu gujewa shaye-shaye a yayin tuki, tare da yawaita gudu fiye da kima.

Inda suka tabbatar da cigaba da fadakar da mambobin su da jama’ar gari domin gujewa samun hadura a fadin kasar nan.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce!
Next Post: Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • Zelensky Na Ukraine Zai Gana Da Takwaransa Na Faransa A Yau Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.