Amurka da Iran sun yarda zasu tattauna gobe Jumma’a a kasar Oman, a cewar jami’an kasashen biyu, sai dai kuma har yanzu ba su cimma daidaituwa a kan nacewar da Amurka take yi cewa lallai tattaunawar ta hada har da makamai masu linzami na Iran, yayin da ita kuma take cewa shirinta na nukiliya kawai zata tattauna akai.
Wannan yunkurin na diflomasiyya yana zuwa a yayin da Amurka take ta girka sojoji a yankin gabas ta tsakiya, su kuma kasashen yankin suke kokarin ganin an kaucewa fadan soja da suke fargabar cewa zai iya yaduwa zuwa fadin yankin.
Sabanin ra’ayi a game da abubuwan da za a tattauna a kai sun janyo tababa a kan ko za a iya yin zaman, abinda zai haifar da yanayin da shugaba Donald Trump na Amurka zai iya yin amfani da shi don aiwatar da barazanarsa ta kai hari a kan Iran.
Jami’an Amurka da na Iran sun ce sassan biyu sun yarda za a gudanar da wannan taron a Muscat, babban birnin Oman, a bayan da tun farko aka ce za a yi ne a Istanbul na Turkiyya.
Amma babu wata alamar dake nuna cewa sun cimma daidaituwa a kan ajandar wannan taron.


