Amurka ta Aike da rundunar sojoji zuwa Nigeria, a cewa janar din sojan da ke kula da harkokin sojin Amurka a Afirka ranar Talata. Wannan shine lokaci na farko da Amurkan ta sanar akwai dakarun ta a kasar tun bayan harin da ta kai ranar 25 ga Watan Disambar bara.
Shugaba Donald Trump ya bada umurni a kai harin ne a wuraren da yake cewa ‘yan ta’adda na labewa a Nigeria, ya kuma ce wasu hare-haren zasu biyo baya.
Janar din sojin Amurkan ya ce, an Aike da dakarun ne bayan kasashen biyu sun cimma yarjejeniya cewar ya kamata a kara daukan matakai don dakile ta’addanci a yammacin Afirka.


