Amurka ta sanar a ranar Laraba cewa ta cire takunkumi da ta kakaba wa shugabar rikon ƙwarya ta Venezuela, Delcy Rodriguez, kamar yadda aka bayyana a shafin Ma’aikatar Kuɗi ta ƙasar. Wannan na zuwa ne kasa da watanni uku bayan sojojin Amurka sun kama tsohon shugaban ƙasar, Nicolas Maduro, a wani samame da suka kai a babban birnin ƙasar.
Gwamnatin Trump ta yi hulɗa sosai da gwamnatin rikon ƙwarya ƙarƙashin jagorancin Rodriguez, wadda tsohuwar mataimakiyar shugaban ƙasa ce kuma abokiyar hulɗar Maduro. Amurka ta aika sakatarorin makamashi da harkokin cikin gida zuwa Caracas, tare da masu zuba jari, ta kuma kulla yarjejeniya da za ta ba Amurka damar sayen man Venezuela.
Haka kuma ta yaba da sauye-sauyen da aka yi a fannonin mai da ma’adinai domin jawo jarin ƙasashen waje, tare da sassauta wasu takunkumi.
A watan Maris, Washington ta amince da Rodriguez a hukumance a matsayin shugabar Venezuela, wanda hakan ya ba gwamnatin ta damar sake buɗe ofisoshin jakadanci tare da sake karɓar ikon kamfanonin Venezuela da ke ƙasashen waje.
Rodriguez ta yi maraba da wannan mataki, inda ta bayyana a wani sako da ta wallafa a shafin X cewa wannan “wani mataki ne na daidaita da ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashenmu.”


