Rundunar sojin kasar Chadi ta gano gawar wani dan yawon bude ido, dan asalin kasar Faransa, wanda ya bace a kwanakin nan a arewa maso gabashin kasar, a cewar hukumomin yankin, inda suka ce farkon bincike ya nuna ya gamu da hatsari ne na fadowa daga kan dutse.
Magajin garin Amdjarass, inda abun ya faru ya ce, rundunar sojin dake jagorantar nemo mutumin sun shaida masa da safiyar ranar Jumu’a cewa An tsinto gawar dan yawon bude idon, kuma ma’aikatan kiwon lafiya a yankin sun tabbatar da rasuwar sa.
Wani jami’i a ma’aikatar yawon bude ido ta kasar, ya ce akwai yiwuwar fadowar da mutumin yayi daga saman dutse ne yayi sanadiyyar rasuwar sa. Ma’aikatar harkokin kasashen waje ta Faransa tace tana ganawa da hukumomin Chadi bayan da wani dan kasar ta ya bace a wani biki da ake yi kusa da garin Amdjarass.


