A ranar Larabar ne aka kai hari kan babbar tashar iskar gas ta Pars a kasar Iran, wannan shine karon farko na kai hari kan kayayyakin makamashin Iran a mashigin tekun Fasha tun fara yakin Amurka da Isra’ila, lamarin da ya sa Tehran ta gargadi makwabtanta cewa za a kai hari kan na’urorin makamashin nasu “a cikin sa’o’i masu zuwa”.
Tashar Pars dai itace tashar iska mallakar Iran da take mafi girman tashar gas a duniya, wanda Iran ta raba da Qatar da ke gabar tekun Gulf. Kamfanin dillancin labaran kasar Iran ya bayar da rahoton cewa, an kai harin tankunan gas da wasu sassan matatar mai, an kwashe ma’aikata zuwa wani wuri don basu kariya, sannan kuma ma’aikatan gaggawa na kokarin kashe gobara.
Kafofin yada labaran Isra’ila sun yi ta yada labarin cewa Isra’ila ce ta kai harin tare da amincewar Amurka. Sojojin Isra’ila ba su amsa bukatar jin ta bakinsu ba.
Qatar, kawayen Amurka dake dauke da sansanin sojin saman Amurka mafi girma a yankin, ta kira harin da Isra’ila ta kai ba tare da ambaton wani rawar da Amurka ta taka ba. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta kira lamarin “mai hadari da rashin da’a” wanda ya jefa tsaron makamashin duniya cikin hadari.
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun shaida wa Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa da Qatar da su kwashe inasu-inasu a wasu wuraren samar da makamashi.


