A ranar Litinin shugaban rajin kare hakkin Majalisar Dinkin Duniya Volker Turk, ya ce hare-hare dake kashe mutane daga jirage mara matuki na drone suna ci gaba da afkuwa duk da rundunar sojojin Sudan sun kawo karshen mamayar da ‘yan tawayen RSF suka yi a biranen dake kudancin kasar.
Rundunar sojan Sudan sun ce sun kawo karshen kawanyar da dakarun ‘yan tawayen suka yiwa birnin al-Delani karshen watan Janairu, garin Kadugli kuma a farkon wannan watan, inda mazauna wajen suka sha fama da yunwa da rashin isassun magunguna saboda toshe hanyoyin shigowa da kayayyaki da ‘yan tawayen suka yi.
Amma duk da nasarar kwato biranen daga hannun ‘yan tawaye, duka bangarorin biyu na ci gaba da kai hare-hare ta jirage marasa matuki na drone, da yayi sanadiyyar rayuka, da kuma jikkatar fararen hula da dama, a cewar Mr Turk, lokacin da yake bayani ga Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya, a wata tattaunawa kan kasar Sudan a Geneva.


