An gudanar da sallar roƙon ruwa a Saudiyya saboda ƙarancin ruwa da tsananin zafi dake kasar take Fuskanta.
A safiyar yau, Alhamis, an gudanar da sallar roƙon ruwa (Salat al-Istisqa) a wurare daban-daban a faɗin ƙasar Saudiyya, bisa umarnin hukumomin addini da gwamnati, domin neman rahamar Allah bayan dogon lokaci ba tare da samun ruwan sama ba.
Dubban jama’a sun halarci sallar a masallatai da filayen idi a manyan birane kamar Riyadh, Makkah, Madinah, da Dammam, inda aka yi addu’o’i na musamman domin Allah Ya sauƙar da albarkar ruwan sama, Ya kuma dawo da nutsuwa ga ƙasa da mazaunanta.

Rahotanni sun nuna cewa ƙasar na fuskantar matsalar tsananin zafi da ƙarancin ruwa, wanda ya shafi amfanin gona da rayuwar jama’a. Hukumomi sun buƙaci al’umma da su ci gaba da yin istigfari da roƙon gafarar Allah, tare da yin addu’a domin samun sauƙi da rahamarsa
A cewar malamai, irin wannan salla na daga cikin hanyoyin da Manzon Allah (SAW) ya koyar domin neman taimakon Allah lokacin fari ko matsalar yanayi.


