Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka
Published: March 2, 2026 at 7:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yakin da Isar’ila da Amurka suke fafatawa da kasar Iran ya ci gaba ya kara tsamari a ranar Litinin, kuma ba’a ga alamar karshen sa ba. Isra’ila ta kaiwa kasar Lebanon hari, tana mai da martani ga harin da kungiyar Hezbollah suka kai mata.

Ita kuwa fadar Tehran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuki na drone zuwa kasashen tekun fasha, da filin sansanin sojin sama na Bahrain, har can zuwa kasar Cyprus.

Kasar Kuwait kuwa ta harbo jiragen yakin Amurka bisa kuskure, dukkanin mutane 6 na cikin jiragen sun tsira da ran su. Wani hoton bidiyo da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya yarda da sahihancin sa ya nuna daya daga cikin jiragen yana yin kasa yayin da injin sa ke kamawa da wuta.

Har ila yau Amurkan ta ce Sojojin ta 4 sun mutu, amma bata bada bayanin ta yadda suka rasa rayukan nasu ba. Wasu jami’an Amurka su biyu sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane 3 na farko da suka rasu an kashe su ne a sansanin soji a Kuwait.

Shugaban Amurka Donald Trump ya ci gaba da kira ga ‘yan kasar Iran da su tashi su hambarar da shugabannin su, kuma ya ce harin da ake kaiwa zai iya shafe makonni. Su kuma shugabanni addini na Iran basu nuna wata alama ta yada Makamai ba.

Wani malamin makaranta a Iran Morteza Sedighi da ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho ya ce harin Amurka da Isra’ila yana kakkashe yara, kuma suna kai hari asibitoci, yace wannan shine demokradiyar da Trump yake so ya kawo mana. Farko hukumomin Iran sun kashe mutanen da basu ji ba basu gani ba, yanzu kuma Isra’ila da Amurka na kashe mutane inji shi.

Afrika, Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci
Next Post: Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
Sojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Bindiga A Kano Da Katsina Tsaro
Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu Afrika
Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
Tsananin Sanyi Ya Kashe Mutane 38 A Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu
  • Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi
  • Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
  • Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.