Yakin da Isar’ila da Amurka suke fafatawa da kasar Iran ya ci gaba ya kara tsamari a ranar Litinin, kuma ba’a ga alamar karshen sa ba. Isra’ila ta kaiwa kasar Lebanon hari, tana mai da martani ga harin da kungiyar Hezbollah suka kai mata.
Ita kuwa fadar Tehran ta harba makamai masu linzami da jirage marasa matuki na drone zuwa kasashen tekun fasha, da filin sansanin sojin sama na Bahrain, har can zuwa kasar Cyprus.
Kasar Kuwait kuwa ta harbo jiragen yakin Amurka bisa kuskure, dukkanin mutane 6 na cikin jiragen sun tsira da ran su. Wani hoton bidiyo da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya yarda da sahihancin sa ya nuna daya daga cikin jiragen yana yin kasa yayin da injin sa ke kamawa da wuta.
Har ila yau Amurkan ta ce Sojojin ta 4 sun mutu, amma bata bada bayanin ta yadda suka rasa rayukan nasu ba. Wasu jami’an Amurka su biyu sun shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane 3 na farko da suka rasu an kashe su ne a sansanin soji a Kuwait.
Shugaban Amurka Donald Trump ya ci gaba da kira ga ‘yan kasar Iran da su tashi su hambarar da shugabannin su, kuma ya ce harin da ake kaiwa zai iya shafe makonni. Su kuma shugabanni addini na Iran basu nuna wata alama ta yada Makamai ba.
Wani malamin makaranta a Iran Morteza Sedighi da ya zanta da kamfanin dillancin labarai na Reuters ta wayar tarho ya ce harin Amurka da Isra’ila yana kakkashe yara, kuma suna kai hari asibitoci, yace wannan shine demokradiyar da Trump yake so ya kawo mana. Farko hukumomin Iran sun kashe mutanen da basu ji ba basu gani ba, yanzu kuma Isra’ila da Amurka na kashe mutane inji shi.


