Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya
Published: January 11, 2026 at 10:06 PM | By: Bala Hassan | Updated: January 11, 2026

CAF Ta fara Bincike Kan Rikicin Bayan tashi a Wasan Algeria Da Najeriya.

Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (CAF) ta fara bincike a hukumance kan munanan abubuwan da suka biyo bayan wasan kwata-final na Kofin Kasashen Afirka tsakanin Algeria da Najeriya a daren Asabar,

A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi, CAF ta tabbatar da cewa ‘yan wasan Algeria da membobin ma’aikatan bangaren masu horaswa sun tunkari alkalin wasan jim kadan bayan an busa tashi a wasan.

An ruwaito cewa lamarin ya kara kamari yayin da wasu daga cikin ‘yan wasan Algeria suka bi alkalan wasa zuwa cikin hanyar tafiyarsa zuwa dakin hutawa da aka tanadar masa, wani abu da CAF ta kira “abin da ba za a yarda da shi ba” kuma ya saba wa dokokin ladabtarwa na gasar.

CAF ta kuma bayyana cewa tana duba rahotannin rikicin da ya shafi ‘yan jarida da sauran ma’aikatan kafofin watsa labarai bayan tashi a wasan, yayin da tashin hankali ya bazu a wajen filin wasa.

Wasan Algeria da Najeriya, wanda aka buga a Marrakech, ya ƙare da 2-0 nasara ga Super Eagles, ta Najeriya sakamakon da ya haifar da yanayin hayaniya daga sansanin Algeria.

Hukumar ta tabbatar da cewa za a yi nazari sosai kan dukkan rahotannin wasanni, na gabatar da alkalan wasa, da kuma shaidun bidiyo a matsayin wani bangare na binciken.

CAF ta kara da cewa za a sanar da matakan ladabtarwa da suka dace da zarar an kammala binciken.

Wannan lamari na ci gaba da kara haifar da cece-kuce a wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin zakarun Afirka, yayin da AFCON 2025 ke shirin shiga mataki mai muhimmanci na wasan dab da karshen.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Mun Ware Biliyan 42 Don Inganta Lafiyar ‘Yan-Kasa
Next Post: Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku

Karin Labarai Masu Alaka

An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
Okoye Na Shirin Maye Gurbin Nwabali, AFCON 2025: Wasanni
Ronaldo Da Messi Ka Iya Hadu A Gasar Cin Kofin Duniya: Ta Ya Ya ? Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
  • Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne Amurka
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba Labarai
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.