Dakarun gwamnatin kasar Sham sun kame lardukan da ke arewaci da gabashin kasar gam bayan ficewar dakarun kurdawa cikin gaggawa, a wani yanayi da ya bada mamaki, wanda kuma ya kara karfafa mulkin shugaba Ahmed al-Sharaa.
Dakarun kurdawa sun yarda da ficewa daga yankunan Aleppo, da suka dade suna rike da madafun ikon su, har da wurare masu arzikin man fetur, ranar Lahadi bayan da aka shafe kwanaki ana gwabza kazamin fada tsakanin su da dakarun gwamnati.
Amma duk da Wannan matsayar da aka cimma don kawo zaman lafiya, rahotanni sun nuna cewa An ci gaba da gwabza fada ranar Litinin.
Dakarun kurdawa na SDF sun watsu dauke da Makamai sun far ma wani gidan kurkuku da suke tsare da dubbannin ‘yan kungiyar ta’adda na ISIS, ba tare da sun fadi sunan wadanda suka kai harin ba. Kurdawan sun kara da cewa suna Karawa da dakarun gwamnati kusa da wani kurkukun da ke dauke da ‘yan ISIS kusa da garin Raqqa.
A nasu bangaren, sojojin Syria sun zargi dakarun Kurdawan da neman kawo koma baya a yarjejeniyar da aka yi, inda suka ce An kashe sojojin su 3 a fadan na kwanan nan


