Tarique Rahman, wanda ya shafe shekaru 17 yana gudun hijira da ya kakabawa kan sa, yanzu na gab da rike ragamar mulkin Bangladesh.
Zaben da aka gabatar ranar Alhamis ya nuna cewa jam’iyyar Tarique Rahman ta Nationalist wato BNP ta lashe mafi yawan kujeru, a cewar kafafen yada labarai na kasar. Ita ma da kan ta jam’iyyar BNP ta yi ikirarin lashe zaben.
Tarique Rahman, mai shekaru 60 a duniya ya koma kasar sa ne daga birnin London, kwanaki bayan mahaifiyar sa, kuma tsohuwar prime ministan Bangladesh ta rasu sakamakon doguwar jinya. A zaben ya fuskanci jam’iyyar addini mai tasowa, mai ra’ayin mazan jiya, wadda ta yi suna tun bayan tashin-tashinan da yayi sanadin hambarar da prime minista Sheikh Hasina.
Duk da wannan nasara da Tarique Rahma ya samu, yana da jan aiki nan gaba a kasar da ta fuskanci tashin hankali tun bayan rigingimun da aka yi a shekarar 2024, har zuwa ranar Alhamis da aka gudanar da zabe.


