Shugaban kungiyar dillalan mai a Kenya ya gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa daruruwan dillalan mai suna fuskantar karancin mai sakamakon yakin hadin guiwar Amurka da Isra’ila kan Iran, ya kara da cewa kamar kashi 20 cikin dari na dillalai ne suke Fuskantar matsalar, bayan da hukumar kayyade farashin mai ta tsaida farashi duk da cewa farashin ya tashi a fadin duniya.
Babu mamaki idan dillalan mai suka fara boye mai, saboda tsammanin farashinsa zai tashi cikin watan gobe, inji Martin Chomba, shugaban kungiyar dilalan mai masu zaman kansu a Kenya.
Kasashen Afirka suna daga cikin wadanda wannnan matsalar yakin tafi shafa ta fuska biyu, daga na karancin mai da kuma tashin farashi, Sakamakon kasa jigilar mai a mashigin ruwan Hormuz, inda ta nan ne kashi 20 cikin dari na mai da iskar gas da duniya take amfani dashi suke bi.


