Jam’iiyyar ADC Ta Bukaci A Sauke Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Amupitan
Gamayyar adawa ta jam’iyyar ADC ta bukaci murabus ko a sauke shugaban hukumar zaben Najeriya INEC Joash Amupitan da kwamishinoninsa daga mukaminsu don ba su da kwarin guiwar za su gudanar da zabe mai adalci.
Bukatar ta fito ne a taron gaggawa na manyan ‘yan adawar karkashin jagoransu tsohon shugaban majalisar dattawa David Mark.
“mu na bukatar murabus ko a sauke shugaban hukumar zabe da kwamishinoninsa don ba mu amince za su iya yi ma na adalci a babban zaben 2027 ba” Inji shugaban hadakar David Mark wanda ke martani mai zafi bayan matakin INEC na dakatar da amincewa da bangarori biyu masu da’awar hakkin shugabancin jam’iyyar.
INEC ta ce ta bi umurnin kotu ne wajen dakatar da karbar bayanai daga shugaban hadakar David Mark da kuma na bangaren turjiya Nafiu Bala sai an samu sabon umurnin kotu.
Mark ya ce ya kamata INEC ta jira sai kotun daukaka kara ta yi matsaya kan takaddamar, amma maimakon haka sai INEC ta bi muradun jam’iyyar APC mai mulki.
A nan Mark ya ce sun sanar da INEC gudanar da tarukan jam’iyya daga 9 ga watan nan na Afrilu inda zai karkare da babban taro ranar 14 ga wata, kuma za su cigaba da wannan shiri ba fashi.
Babban jigon hadakar tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya ce su na son lallai INEC ta yi adalci.
Ita ma shugabar mata ta jam’iyyar Na’omi Abel ta ce akwai kalubale ga hanyar da ta ce an dauka ta maida Najeriya kasa mai bin jam’iyya daya.
In za a tuna shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa ba ta sha’awar maida Najeriya kasa mai bin jam’iyyar daya.
A babban taron jam’iyyarsa ta APC, shugaba Tinubu ya ce ya yi amanna da tsarin gasa a harkokin dimokradiyya.
Za a zuba ido kan kotu da hukumar zabe don ganin ko akwai sauyin da za a iya samu yayin da kulle-kulle ko rashin jituwa ya jefa sufana a tayar ADC.
Wannan ba ma abun mamaki ba ne, don APC ma ta sha da kyar kan hatta sunanta gabanin zaben 2015 zamanin mulkin tsohon shugaba Jonathan da tsohon shugaban hukumar zabe Farfesa Attahiru Jega.

