Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus
Published: April 3, 2026 at 7:21 AM | By: Nasiru Adamu Elhikaya

Jam’iiyyar ADC Ta Bukaci A Sauke Shugaban Hukumar Zaben Najeriya Amupitan

Gamayyar adawa ta jam’iyyar ADC ta bukaci murabus ko a sauke shugaban hukumar zaben Najeriya INEC Joash Amupitan da kwamishinoninsa daga mukaminsu don ba su da kwarin guiwar za su gudanar da zabe mai adalci.

Bukatar ta fito ne a taron gaggawa na manyan ‘yan adawar karkashin jagoransu tsohon shugaban majalisar dattawa David Mark.

“mu na bukatar murabus ko a sauke shugaban hukumar zabe da kwamishinoninsa don ba mu amince za su iya yi ma na adalci a babban zaben 2027 ba” Inji shugaban hadakar David Mark wanda ke martani mai zafi bayan matakin INEC na dakatar da amincewa da bangarori biyu masu da’awar hakkin shugabancin jam’iyyar.

INEC ta ce ta bi umurnin kotu ne wajen dakatar da karbar bayanai daga shugaban hadakar David Mark da kuma na bangaren turjiya Nafiu Bala sai an samu sabon umurnin kotu.

Mark ya ce ya kamata INEC ta jira sai kotun daukaka kara ta yi matsaya kan takaddamar, amma maimakon haka sai INEC ta bi muradun jam’iyyar APC mai mulki.

A nan Mark ya ce sun sanar da INEC gudanar da tarukan jam’iyya daga 9 ga watan nan na Afrilu inda zai karkare da babban taro ranar 14 ga wata, kuma za su cigaba da wannan shiri ba fashi.

Babban jigon hadakar tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya ce su na son lallai INEC ta yi adalci.

Ita ma shugabar mata ta jam’iyyar Na’omi Abel ta ce akwai kalubale ga hanyar da ta ce an dauka ta maida Najeriya kasa mai bin jam’iyya daya.

In za a tuna shugaba Tinubu ya ce gwamnatinsa ba ta sha’awar maida Najeriya kasa mai bin jam’iyyar daya.

A babban taron jam’iyyarsa ta APC, shugaba Tinubu ya ce ya yi amanna da tsarin gasa a harkokin dimokradiyya.

Za a zuba ido kan kotu da hukumar zabe don ganin ko akwai sauyin da za a iya samu yayin da kulle-kulle ko rashin jituwa ya jefa sufana a tayar ADC.

Wannan ba ma abun mamaki ba ne, don APC ma ta sha da kyar kan hatta sunanta gabanin zaben 2015 zamanin mulkin tsohon shugaba Jonathan da tsohon shugaban hukumar zabe Farfesa Attahiru Jega.

 

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/04/ADC-VOWS-TO-GO-AHEAD-WITH-CONGRESSES-CALL-ON-AMUPITANS-SACK.mp3

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Hukumar ‘Yan Sanda Sun Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
Putin, Sakon Sabuwar Shekara Ya Jinjinawa Dakarun Rasha Da Suke Yaki A Ukraine Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus
  • Hukumar ‘Yan Sanda Sun Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe
  • Kasar Congo Ta Kawo Karshen Cutar Kyandar Biri
  • Mutane 15 Sun Rasa Rayukan Su A Gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kwango
  • Kungiyoyi Sunyi Kasashen Jinkiri A Bunkasar Tattalin Arzikin Kashen Afirka

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Nasarawa Ce Zakara A Wasan Kwallon Kafa Ta Kurame 2025 Wasanni
  • Masoya Kungiyar Kwallon Kafar Morocco Suna Cikin Farin Ciki Bisa Hukuncin Kotu Afrika
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Sham Ta Sallami Wasu Fararen Hula Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.