Ghana zata yi watsi da duk wata yarjejeniyr da kasar ta kulla kan hakar ma’adinai ta kuma ninka harajin da take karba a wannan fanni, wani gagarumin garambawul da hukumar kula da hakar zinari ko Gold da turanci, wacce itace akan gaba wajen hako wannan ma’adanai a duk fadin Afirka kasar ta dauki wadannan matakan ne da zummar cin gajiyar tashin farashin zinari a duuniya.
Waɗannan sauye sauye suna daga gagarumin garambawul da nufin karfafawa masu zuba jari guiwa da burin gwamnati na samun moriya daga hakar ma’adinai, inji mukaddashin shugaban hukumar Isaac Tandoh ya fada a hira da aka yi dashi a birnin Accra.
A Ghana, wacce itace ta shida a duniya a arzikin zinari, galibi yarjejeniyoyin nan ana kulla su na tsawon shekaru 5-15, kan haraji da gwamnati zata karba, su kuma kamfanoni masu hako ma’adinai za su zuba jari na dala milyan 300 zuwa Miliyan dari biyar, domin gina ramukan hakar ma’adinai da fadada su.
Haka nan tilas kamfanonin su tsawaita amfani da wuraren hakar ma’adinai da kamar shekaru uku, kuma su kara yawan abunda suke hakowa da kamar kashi 10, wadandan suna daga cikin sharuddan neman sabunta yarjejeniya.
Da aka nemi jin ta bakinsu kan wadannan sauye sauye manyan kamfanonin hakar Zinari biyu a Ghana basu ce uffan ba kan wannan canji.


