A zaman Majalisar Zantaswar jihar Gombe Karo na 53 Gwamna Inuwa Yahaya ya rusa Majalisar Zartarwa ta Jihar a yau laraba 08 Afrilun 2026
“Mun rusa majalisar zartarwa ta jiha ne don baiwa kwamishinonin mu dake da sha’awar takara a zaben 2027 dake tafe dama su cinma muradun su na siyasa. Bayan kwamishinoni Kazalika na bada umurni wa duk masu mukamai na siyasa a matakai daban daban dake sha’awar takara a zaben dake tafe da su ajiye aikin su daga nan zuwa 10th April, 2026 don cinma burin su na takara a mukaman da suke muradin nema. Ina musu godiya maras adadi sabida rawar da suka taka wajen nausa gwamnatin mu gaba cikin kusan shekaru uku da mukayi a zangon gwamnati na na biyu”
Gwamna Inuwa Yahaya biyo bayan rusa majalisar zartarwa ta jiha da yayi.



