Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote
Published: April 1, 2026 at 3:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 1, 2026

Gwamnatin tarayyar Najeriya da ta jihar Kano da kuma gidauniyar rukunin kamfanonin Dangote, sun cimma yarjejeniyar haɓakawa, tare da kula da babbar cibiyar koyon sana’o’i ta Dangote (Dangote Ultramodern Skills Acquisition Center) da ke birnin Kano.

Wannan mataki dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Hukumar Ilimin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano (STSB), Farfesa Dahiru Sale Mohammed, ya fitar a madadin Kwamishinan Ilimi na jihar.

A karkashin wannan sabuwar dangantaka, ɓangarorin uku za su dauki nauyin garambawul da inganta kayan aikin cibiyar, sannan su tabbatar da dorewar ayyukanta na tsawon shekaru 20 masu zuwa.

Cibiyar, wacce aka gina domin bai wa matasa horo kan kwarewar hannu da fasahar zamani, ana sa ran za ta kasance kashin baya wajen rage radadin rashin aikin yi a jihar ta Kano da ma makwabtanta.

Farfesa Dahiru Sale ya bayyana cewa wannan yunkuri zai tabbatar da cewa cibiyar ba ta durkushe ba kamar yadda wasu ayyukan ke yi idan aka samu canjin gwamnati, duba da tsarin kula da ita na dogon lokaci da aka kulla.

Jihar Kano dai ita ce jiha mafi yawan jama’a a arewacin Najeriya, inda matasa ke da kaso mafi tsoka. Wannan cibiya za ta mayar da hankali ne wajen koyar da sana’o’in da suka dace da bukatun karni na 21, domin ba wa matasa damar dogaro da kansu maimakon jiran aikin gwamnati.

Sanarwar ta jaddada cewa an kammala dukkan shirye-shiryen fara aikin fito da sabuwar fuskar cibiyar nan ba da jimawa ba.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya
Next Post: Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
Shugaban Amurka Ya Sauke Antoni Janar Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas Labarai
  • Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
  • Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.