Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Soji A Nijar Ta Hana Fitar Da Albarkatun Kasa
Published: November 29, 2025 at 8:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 29, 2025

Kamfanin Orano ya sanar cewa hukumomn Nijar sun fara aiyukan fitar da ton ton na Uranium daga garin Arlit zuwa waje ba tare da sanar da shi ba. Matakin da kamfanin na Faransa ya ce ya saba wa umurnin kotun bankin duniya, wace ta bukaci bangarorin su jira ta kammala shari’ar da ke gabanta.
Kawo yanzu ba wata sanarwa daga bangaren gwamnatin Nijar  sai dai kwararru kan sha’anin ma’adanai sun fara bayyana matsayinsu.
A kalla ton 1300 na Uranium ne ke jibge a kamfanin SOMAIR da ke Arlit na arewacin Nijar bayan da gwamnatin kasar ta dakatar da fitarwa zuwa waje a washegarin juyin mulkin Yulin 2023, saboda abin da suka kira rashin haske daga kamfanin Orano da ke harkar Uranium shekaru sama da 50.
Dangantaka ta ci gaba da tsami a tsakanin bangarorin biyu abin da ya sa Orano shigar da kara a kotun CIRDI domin ta shiga tsakani. A yayin da ake jiran matsayin kotun kamfanin na Faransa ya sanar cewa motoci dauke da lodin Uranium sun fara dagawa daga Arlit zuwa Agadez a yunkurin Isa gabar teku. Kwararre kan sha’anin albarkatun karkashin kasa Mahamadou Tchiroma Aissami na fassara abin a matsayin ci gaban takaddama.
Kamfanin na Orano ya ce fitar da Uranium a wannan lokaci ya saba wa umurnin kotu. sai dai ‘yan Nijar irinsu masani a harakar makamashi injiniya Rabiou Malan Issa na ganin koma mai ake ciki Nijar ce uwar gijiyar albarkatun da ake rikicin kan su.
 Nijar na daga cikin kasashen da suka rattaba hannu kan yarjeniyoyin hakar ma’adanai da hanyoyin sayar da su a kasuwannin duniya, dalili kenan wadanda suka lakanci fannin ke gargadin mahukunta a kan hanyoyin mafita.
 Jamhuriyar Nijar na daga cikin kasashen da suka fi kowa yawan Uranium a duniya sai dai alamu na nunin kasar da al’ummarta ba su amfana da arzikin, kamar yadda ya dace abin da ya sa gwamnatin CNSP ta dage da yunkurin sabunta abokan hulda a wannan fanni kuma bayanai na cewa kamfanin ROSATOM na Russia na daga cikin masu fatan ganin an ba su dama.
Afrika

Post navigation

Previous Post: Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed
Next Post: Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba!

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe Najeriya
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • Gwamnatin Janhuriyar Nijar Ta Soke Lasisin Wasu Kamfanonin Dakon Mai Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.