A ranar Talata ne ‘yan sanda a Najeriya suka tuhumi Tsohon ministan shari’a, Abubakar Malami, tare da dan sa Abdulaziz da laifuffukan da suka jibanci ta’addanci da muggan makamai watanni bayan da hukumar hana wadaka da kudin jama’a, wato EFCC ta tuhume shi da laifin halatta kudaden haram.
Masu gabatar da kara sun yi ikirarin cewa, a watan Nuwambar shekara ta 2022, Malami ya tallafawa ta’addanci da sanin sa ta hanyar kin hukunta masu daukan nauyin ‘yan ta’adda, wadanda aka gabatar da takardun karar su a gaban sa, lokacin da yake rike da mukamin Antoni janar na kasa.
Malami da dan sa duk sun musanta zargin da ake musu, kuma hukumomi zasu ci gaba da tsare su, kafin a fara zaman kotu ranar 20 ga Watan Fabrairu, bayan da aka ki basu beli.


