Jami’an DSS sun kama tsohon ministan ne jim kadan da barin Gidan Gyaran Hali na Kuje, bayan kammala sharuddan belin sa.
Manema labarai sun ruwaito cewa tsohon Babban Lauyan yana fuskantar sabon bincike daga hukumar tsaron farin kaya.
An gano cewa jami’an Hukumar EFCC sun samu makamai a gidan Malami da ke Kebbi yayin wani bincike da suka gudanar.
A baya-bayan nan, tsohon Babban Lauyan ya zargi DSS da shirin sake kama shi daga gidan gyaran hali na Kuje.
Wata Kotun Tarayya a ranar Laraba ta bayar da belin Malami, matar sa da dan sa, kan kudi Naira miliyan 500 kowannen su, tare da mutane biyu da za su tsaya musu.
Sai dai, a wata sanarwa da Mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Mohammed Bello Doka, ya fitar, tsohon ministan ya zargi DSS da sanya ido a gidan gyaran hali domin sake kama shi.
Rahotanni sun nuna cewa Malami ya cika dukkan sharuddan belin sa, amma duk da haka jami’an tsaro sun sake kama shi.


