Iran tace Isra’ila ta kai hari kan cibiyar makamashin nukiliyan ta na Ahmadi Roshan a Natanz a safiyar Asabar. Kwararru a bangaren fasaha sun ce babu alamar digar guba daga makamashin, kuma mazauna kusa da wurin basa cikin hadari. Isra’ila tace bata da masaniya kan harin, yayin da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) tace tana bincike kan abun.
Kafar yada labarai ta Iran ta kuma ce an kai hari wata tasha, a tashar jirgin ruwa dake kudancin Bushehr, da kuma wani jirgi da ba kowa cikinsa a tsibirin Kharg, tsibirin da Iran take lodin kusan duka man da take fitarwa da shi, wurin da ake gani Amurka zata farma idan tayi niyyar kai harin kan cibiyoyin makamashi na Iran, ko tayi amfani da sojin kasa don kwace shi.


