Shugaban addini Islama na Iran, Ayatollah Ali Khameni, yace ba zai bada kai ba, bayanda shugaban Amurka Donald Trump yayi barazanar zai kai dauki ga ‘yan kasar da suke zanga zanga, a dai dai lokacin da kungiyoyin kare hakkin Bil’adama a Farisan, suke bada labarin hukumomi sun zafafa kame, bayan da aka shafe kwanaki mutane suna zanga zanga saboda tashin farashin kayayyaki.
Da yake magana a wani lamari ranar Asabar, Khameni yace, jamhuriyar Farisa mai bin tafarkin Islama, “ba zata sakarwa makiyinta ba,” kuma ayi maganin masu zanga zanga.”
Kafofin yada labaran kasar, sun bada rahoton mutuwar mutane uku a ranar Asabar, yayinda kungiyoyin kare hakkin Bil’adama suka ce mutane akalla 10 ne suka mutu a duk fadin kasar tun ranar lahadi data gabata, yayinda darajar kudin kasar yayi mummunar faduwa a yayinda tattalin arzikin kasar ke fama da takunkumai.


