Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11 Afrika
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika

Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora
Published: April 6, 2026 at 7:32 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta sanar cewa za ta karɓi ‘yan ƙasashen waje da Amurka ke korar su daga ƙasar, ƙarƙashin wata sabuwar yarjejeniya da gwamnatin Donald Trump, kamar yadda gwamnati a Kinshasa ta bayyana a cikin wata sanarwa jiya Lahadi.

Gwamnatin ta ce za ta fara karɓar waɗanda aka kora daga watan Afrilu, amma ba ta bayyana adadin mutanen da ta amince za ta karɓa ba.

Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka ce za ta ɗauki nauyin wannan shiri gaba ɗaya, ba tare da wani kuɗi daga gwamnatin Kongo ba. Haka kuma, an tanadi wuraren zama kusa da babban birnin ƙasar, wato Kinshasa, domin sauƙaƙa wa waɗanda za a kawo masauki.

Amurka ta riga ta tura wasu ‘yan ƙasashen waje da aka kora zuwa wasu ƙasashen Afirka da suka haɗa da Ghana, Cameroon, Equatorial Guinea da Eswatini, lamarin da ya janyo suka daga masana harkokin doka da kuma ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam.

Wannan yarjejeniya na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin Trump ke ƙoƙarin aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Kongo da Rwanda, tare da wata yarjejeniya da ke tabbatar da samun damar Amurka ga muhimman ma’adanan Kongo.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Rundunar Sojin Najeriya Ta Kubutar Da Wasu Mutane 31 Da Aka Yi Garkuwa Dasu
Next Post: Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran

Karin Labarai Masu Alaka

Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa Afrika
Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya
  • Tinubu Ya Lashe Zaɓen Fidda Gwanin APC Da Kuri’u Miliyan 11
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
  • Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.