Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka

Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a
Published: December 3, 2025 at 5:57 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Shugabannin Fulani a Jihar Nejan Nigeria sun koka akan yadda suka ce Jami’an Tsaron ‘Yan-banga na cin zarafin Fulanin ba tare da tantance mai laifi ko mara laifi.

Wannan dai yana zuwa ne bayan da aka yi zargin wasu ‘yan bindiga a yankin karamar Hukumar Mashegu sun ci zarafin shugaban kungiyar makiyaya ta Miyatti Allah tare da wasu Fulanin su 13.
Bayanai dai sun nuna cewa ‘yan bangan sun yima wadan nan Fulani daurin goro tare da gana musu azaba da a yanzu haka suna karbar magani a babbar Asibitin Gwamnati dake Kontagora,
Alh. Muhammadu Mabbe, shine shugaban Fulanin na karamar Hukumar Magama da ya shiga hannun wadan nan ‘Yan banga da a yanzu haka yake kwance cikin wani mawuyancin hali, yace ‘yan bangar sun sameshi a kofar gidan Sarkin koso ne a dai dai lokacin da suke kokarin jana’izar wani yaron su da aka kashe.
Shugaban Babban Jami’i a Ma’aikatar Kula da Harkokin Makiyaya ta Jihar Neja Malam Ababakar Kamfanin Bobi yayi karin haske akan irin azabar da aka basu.
Sarkin Fulanin Minna Alhaji Hasan Shiroro, wanda shima a kwanakin baya yace ‘yan bangar sun bindige yaro kuma nan take ya mutu har lahira.
Mun tuntubi shugaban ‘yan bangar na Jihar Neja Nasiru Muhwmmad Manta, yace basu da hannu a ciki, amma kuma zasu gudanar da bincike akan lamarin.
Tini dai masu kare hakkin dan adam suka bayyana damuwa akan wannan lamari Kwamrade Kabiru Idris Jami’i ne a hukumar kare hakkin dan adam ne a Jihar Nejan, inda yace basu yadda da wannan cin zarafin ba.
Suma masana a fannin tsaron da zamantakewa suka nuna bukatar dakatar da irin wannan daukar doka a hannu, don shawo kan matsalolin tsaro da Najeriya ke fama dashi.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu
Next Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mali Da Burkina Faso Za Su Haramta Wa Amurkawa Izinin Shiga Ƙasashen Su Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwamitin Aikin Hajjin Najeriya Ya Shigar Da Korafi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • Kasashe 5 Da Ke Fama Da Matsanancin Zazzabin Cizon Sauro Rediyo
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.