Ma’aikatar Muhalli ta Tarayyar Najeriya ta zaɓi jihar Kano domin aiwatar da shirin gwajin Bunƙasa Dabino da King Salman Humanitarian Aid and Relief Centre (KSrelief) ta gabatar.
Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar Kano, Dakta Dahir M. Hashim, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano bayan karɓar baƙuncin wakilan KSrelief.
Hashim ya ce an zaɓi Kano ne saboda yanayin ta mai dacewa da noman dabino da kuma muhimmancin dabino a al’ada da addini a cikin al’umma.
Ya bayyana cewa shirin zai yi amfani da sabbin dabarun shuka tare da haɗa ƙwararru daga Saudiyya da kuma masana daga Jihar Kano domin tabbatar da zurfin ilimi da musayar ƙwarewa.
Dakta Hashim ya lura cewa shirin ba wai na shuka itatuwa kaɗai ba ne, illa dai wani cikakken aikin raya ƙasa ne da ke da amfani ta fuskar muhalli, tattalin arziki da zamantakewa.
Ya kuma buƙaci tawagar da ta zo da ta tabbatar da haɗa al’umma sosai domin ƙarfafa mallaka da dorewar shirin a nan gaba.
A ƙarshe, ya sake jaddada cewa ma’aikatar a shirye take ga duk wata haɗin gwiwa mai inganci da za ta ƙarfafa juriya da samar da hanyoyin samun abin yi ga al’umma.


