Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Anyi Sallar Rokon Ruwa A Saudiya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika

Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano
Published: February 15, 2026 at 1:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatar Muhalli ta Tarayyar Najeriya ta zaɓi jihar Kano domin aiwatar da shirin gwajin Bunƙasa Dabino da King Salman Humanitarian Aid and Relief Centre (KSrelief) ta gabatar.

Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar Kano, Dakta Dahir M. Hashim, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Kano bayan karɓar baƙuncin wakilan KSrelief.

Hashim ya ce an zaɓi Kano ne saboda yanayin ta mai dacewa da noman dabino da kuma muhimmancin dabino a al’ada da addini a cikin al’umma.

Ya bayyana cewa shirin zai yi amfani da sabbin dabarun shuka tare da haɗa ƙwararru daga Saudiyya da kuma masana daga Jihar Kano domin tabbatar da zurfin ilimi da musayar ƙwarewa.

Dakta Hashim ya lura cewa shirin ba wai na shuka itatuwa kaɗai ba ne, illa dai wani cikakken aikin raya ƙasa ne da ke da amfani ta fuskar muhalli, tattalin arziki da zamantakewa.

Ya kuma buƙaci tawagar da ta zo da ta tabbatar da haɗa al’umma sosai domin ƙarfafa mallaka da dorewar shirin a nan gaba.

A ƙarshe, ya sake jaddada cewa ma’aikatar a shirye take ga duk wata haɗin gwiwa mai inganci da za ta ƙarfafa juriya da samar da hanyoyin samun abin yi ga al’umma.

Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani

Karin Labarai Masu Alaka

An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC Najeriya
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi
  • Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Rasha Takai Sabbin Hare-Hare Akan Wasu Biranen Ukraine Tsaro
  • Kocin Ranchers Bees Ya Yi Murabus Wasanni
  • Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
  • Sojoji Sun Murkushe ‘Yan Bindiga A Jihar Sakkwato Labarai
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Karu A Karshen 2024 Rediyo
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.