Ranar lahadi gwamnatin kasar Sham ta bada sanarwar shirin tsagaita wuta a tsakaninta da dakarun kungiyar SDF ta Kurdawa, a bayan da ta kwace ikon kusan dukkan kasar tare da murkushe dakarun SDF da suka shafe fiye da shekaru 10 suna rike da yankin arewa maso gabashin kasar.
A farkon watan nan ne rikici ya barke a tsakanin dakarun sassan biyu, inda gwamnati ta kai farmaki ta doshi gabashin kasar. Da alamun dakarun kungiyar SDF sun janye a bayan fadan da aka yi ta gwabzawa a lardin Aleppo na gabashin kasar.
Sa’o’i kadan a bayan da gwamnati ta bada sanarwar tsagaita wutar, shugaban kungiyar SDF, Mazloum Abdi, ya tabbatar da hakan cikin wani sakon da ya bayar ta bidiyo, inda yake cewa kungiyarsu ta yi na’am da wannan yarjejeniya wadda ta bukaci janyewarsu daga lardunan Raqqa da Deir el-Zour domin kawo karshen zub da jinin da ake yi.


