Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela
Published: January 3, 2026 at 8:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 3, 2026

Game da Hambarar da Mulkin Shugaban Kasar Venezuela Hukumomin duniya kuma, sunce “Wannnnan matakin ya kasance misali mai hadari, kan yadda za’a gudanar da al’amura nan gaba” inji kakakin sakataren MDD Antonio Gutierrez, ya ci gaba da cewa, sakataren na MDD yana jaddada muhimancin dukkan kasashen duniya su su mutunta dokokin kasa da kasa, ciki harda sharudda da dokokin MDD.

Mr. Gutierrez inji mai magana da yawunsa, yana nuna matukar damuwa cewa anan dai ba’a mutunta dokokin kasa da kasa ba.”

A nata bangaren Jamus ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Muna kira ga duk wadanda wannan lamari ya shafa, su gujewa ruruta wannan yanayi, kuma su nemi hanyoyin hannyoyin warware wannan batu ta fuskar siyasa,” Ta kara da cewa, Venezuela tana bukatar ko ta cancanci zaman lafiya, da tafarkin demokuradiyya nan gaba.”

China a nata bangaren, ma’aikatar harkokin wajen kasar tace, “Sin ta kadu, kuma tayi Allah wadai da kakkausar lafazi, amfani da karfin soja kan kasa mai ‘yanci, da kuma amfani da karfin soja kan shugaban kasa.”

Shi kuma da yake magana kan wannan lamari, ministan harkokin wajen Faransa yace, “matakin soja da ya kai ga kama shugaba Maduro, ya kaucewa amfani da karfi kamar yadda yake a dokokin kasa da kasa itama faransa ta sake jaddada cewa ba za’a samu zaman lafiya mai dorewa ba, idan aka tilasta shi daga ketare, Faransa tace ‘yan kasa ne kadai za su iya shata makomar su.

Da take magana kan wannan batu, ma’aikatar harkokin wajen Rasha tace, “A safiyar nan, Amurka ta nuna fin karfi ta amfani da karfin soja kan kasar Venezuela, wannan abun damuwa ne matuka, kuma abun Allah wadai ne.

Afirka ta kudu ta bakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, ta bukaci kwamitin sulhu na MDD, yayi zaman gaggawa domin duba wannan lamari.

A kasashe dake Latin Amurka ra’ayoyi shugabannin kasashen sun sha ban ban, wasu suna Allah wadai da matakin, wasu kuma suna san barka.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela
Next Post: Jagoran Kasar Iran Yace Basa Bukatar Tallafin Kasar Amurka

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina Labarai
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.